Shugaban Hamas, Ismail Haniyeh, ya kai ziyara Iran

Shugaban Hamas, Ismail Haniyeh, ya isa Tehran a ranar Talata domin tattaunawa da jami’an Iran kwana guda bayan da Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi ƙira ga tsagaita wuta a yaƙin da Isra’ila ke yi da Gaza.

“Shugaban Hamas Ismail Haniyeh a lokacin ziyararsa a Tehran a ranar Talata zai haɗu da Ministan Harkokin Wajen Iran Hossein Amir-Abdollahian,” kamar yadda kafar watsa labarai ta IRNA ta ruwaito.

Wannan ce ziyara ta biyu da shugaban na Hamas ya kai Tehran tun bayan da Hamas ɗin ta ƙaddamar da hari a Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *