Connect with us

Rasuwa

Shugaban ƙasar Namibia, Hage Geingob, ya rasu

Published

on

Shugaban ƙasar Namibia Hage G. Geingob ya rasu ranar Lahadi a yayin da ake duba lafiyarsa a wani asibiti da ke Windhoek babban birnin ƙasar, a cewar wata sanarwa daga Fadar Shugaban Ƙasa.

Sanarwar wadda mataimakin shugaban ƙasar Nangolo Mbumba ya sanya wa hannu ta ce shugaban ya rasu ne a gaban mai ɗakinsa Madame Monica Geingo da ƴaƴansu.

“Ina mai baƙin cikin sanar da ku cewa shugaban ƙasarmu na Namibia abin ƙaunarmu Dr. Hage G. Geingob, ya mutu yau Lahadi, 4 ga watan Fabrairun 2024 da misalin ƙarfe 12 da minti huɗu a Asibitin Lady Pohamba inda likitocinsa suke kula da lafiyarsa,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta yi ƙira da ƴan ƙasar su kwantar da hankulansu, tana mai ƙarawa da cewa Majalisar Ministoci za ta yi taron gaggawa domin ɗaukar matakin da ya dace.

A watan jiya ne marigayin mai shekara 82 ya bayyana wa ƴan ƙasar cewa an gano yana fama da cutar daji.

Ofishinsa ya sanar cewa zai tafi Amurka domin yin jinya amma zai koma gida ranar 2 ga watan Fabrairu.

An zaɓi Mita Geingob a matsayin shugaban ƙasar Namibia a 2015 kuma yana yin wa’adinsa na biyu kuma na ƙarshe ne kafin rasuwarsa.

A watan jiya ne Shugaba Geingob ya caccaki matakin da Jamus ta ɗauka na goyon bayan “Isra’ila game da kisan ƙare-dangin da take yi wa fararen-hula da ba su da laifi a Gaza.”

KU KUMA KARANTA: Gwamna Buni ya yiwa Gwamna Zulum ta’aziyya kan rasuwar mai magana da yawunsa

Ya ce sukar da Jamus ta yi wa Afirka ta Kudu saboda gurfanar da Isra’ila a gaban Kotun Ƙasa da Ƙasa a kan kisan ƙare-dangin da take yi a Gaza ya “girgiza” ƙasarsa.

Jamus ba ta da ƙimar da za ta kare “gwamnatin Isra’ila bisa kisan kare-dangi da take yi wa fararen-hula da ba su da laifi a Gaza da yankin Falasɗinu da aka mamaye,” in ji Namibia.

”A ƙasar Namibia, Jamus ta gudanar da kisan ƙare-dangi na farko a ƙarni na 20 daga shekarar 1904-1908, inda dubban ƴan ƙasar Namibia da ba su ji ba, ba su gani ba suka mutu cikin wulakanci,” kamar yadda Fadar shugaban ƙasar Namibia ta bayyana a wata sanarwa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti  bayan gajeruwar rashin lafiya.

Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.

Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.

Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Mahaifiyar tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff ta riga mu Gidan Gaskiya.

Mahaifiyar tsohon gwamnan, Hajja Aisa, ta koma ta Mahaliccinta ne a ranar Lahadi a Maiduguri, babban birnin jihar.

Ta rasu tana da shekaru 93, bayan fana da rashin lafiya.

Sanarwar rasuwar ta bayyana cewa za yi jana’izar Hajja Aisa da Azahar ranar Litinin 1 ga watan Yuli, 2024.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Za a yi jana’izar ne a gidant Marigayi Galadima Modu Sheriff d da ke Damboa Road a Maiduguri.
Sanarwar ta kuma roka wa marigayiyar gafara da kuma Aljannatul Firdaus.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like