Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya yi gargaɗi haɗe da jan kunne ga ɗansa Seyi

Published

on

Shugaba Tinubu ya ce baya ga ministocinsa, mutane ƙalilan ne kaɗai ya amince su rinƙa shiga taron zaman majalisar zartarwa na ƙasa (FEC).

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya gargaɗi ɗansa Seyi da wasu mutane da ke fadar shugaban ƙasar su daina shiga taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya wato FEC.

Shugaban ƙasar ya bayyana haka a lokacin taron majalisar a ranar Talata.

Tinubu ya ce ya lura ɗansa Seyi da wasu mutane da ba a amince su shiga taron ba suna shige-da-fice a ɗakin taron a makon jiya a yayin da ake tattaunawa kan muhimman abubuwa da suka shafi ƙasar.

Ya gargaɗe su game da wannan ɗabi’a tare da yi musu hani da aikata hakan.

Shugaban ya lissafo sunayen mutum huɗu waɗanda ya ce su kaɗai ya amince su halarci taron bayan ministocinsa.

A makon da jiya, na lura da wasu mutane suna shige-da-fice a yayin wannan taron, na ga hoton dana Seyi yana zaune a baya.

Ba za a yarda da wannan ba, zan sanar muku mutanen da suka kamata su kasance a nan,” in ji shi.

KU KUMA KARANTA: Iran ta gargaɗi Isra’ila kan ci gaba da kai hari kan Falasɗinawa

Shugaban ya ce waɗanda ya amince su halarci taron sun haɗa da mai ba shi shawara kan harkokin tsare-tsare Hadiza Bala Usman da mai taimaka masa kan bayanai da dabaru Bayo Onanuga da sakatarensa na musamman Hakeem Muri-Okunola da sakatarensa Damilotun Aderemi.

Ya ƙara da cewa waɗannan ne kaɗai ya amince su zauna a taron, sai dai idan shi ya buƙaci wani ya shigo taron.

Tinubu ya kuma gargaɗi Sakataren Gwamnatin Tarayya da kuma Shugaban Ma’aikatan Gwamnati da su kula da abin da ya faɗa kan wannan lamarin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like