Shugaba Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA 

0
205
Shugaba Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA 

Shugaba Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake naɗa Birgediya Janar Buba Marwa mai ritaya a matsayin shugaban hukumar yaƙi da sha da safarar miyagun ƙwayoyi a Najeriya NDLEA.

Shugaban ya sake naɗa Marwa ne bisa jajircewarsa a da a ke samun nasara wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi a Najeriya.

KU KUMA KARANTA: NDLEA a Kano ta kama tabar wiwi da kwalaben Akurkura dubu 8

Bayo Onanuga ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa da ya fitar.

Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ne ya fara naɗa Marwa a matsayin shugaban hukumar a shekarar 2021.

Leave a Reply