No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tinubu ya dakatar da shugaba kuma ko’odineta ta hukumar kula da harkokin zuba jari ta ƙasa (NSIPA) Halima Shehu na wani ɗan lokaci daga muƙaminta.

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dakatarwar da aka yi a gidan talabijin na ƙasa a hukumance a wani shiri kai tsaye a ranar Talata, 2 ga watan Janairu.

Har yanzu ba a tantance takamaiman musabbabin dakatar da ita ba, duba da naɗin da aka yi mata watanni kaɗan da suka gabata.

Sai dai wata majiya na cewa shugaba Tinubu ya dakatar da shugabar ne bisa zargin zamba a hukumar.

KU KUMA KARANTA: Hukumar Shari’a ta dakatar da Alkali kan yanke hukunci ta hanyar da ba ta dace ba

An ce mata ta sauka daga muƙaminta domin ba da damar gudanar da cikakken bincike kan zargin da ake mata.

A halin yanzu, shugaban ƙasar ya naɗa Mista Akindele Egbuwalo a matsayin kodinetan riko na NSIPA, har sai an kammala cikakken binciken da shugaba Tinubu ya bayar.

Ya zuwa yanzu, shi ne kodinetan shirin N-Power na ƙasa, kuma sabon naɗin nasa ya fara aiki nan take.

Tinubu ya naɗa Halima Shehu a watan Oktoba 2023, kuma Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin nata a ranar 18 ga Oktoba, 2023.

Ta yi aiki a matsayin mai kula da shirin Cash transfer na ƙasa, inda ta yi amfani da ƙwarewar aikinta na banki da aikinta don ganin an daidaita shirin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...