No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya cire birnin tarayyar ƙasar Abuja daga tsarin Asusun Ajiya na Bai-ɗaya (TSA)

Tinubu ya ɗauki matakin ne da nufin bayar da dama wajen bunƙasa ci gaban birnin ƙarƙashin jagorancin ministan Abuja Nyesom Wike, domin ba shi ƙarin iko kan kuɗaɗen da birnin ke tarawa.

Ministan Abuja, Nyesom Wike ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a taron manema labarai da ya gudanar ranar Juma’a a Abuja.

Asusun Ajiya na Bai-ɗaya (TSA) tsari ne da gwamnatin tarayya ta ɓullo da shi a 2015, da nufin sanya duka kuɗaɗen shiga da gwamnati ke samu a cikinsa, domin tabbatar da gaskiya da bin diddigin kuɗaɗen gwamnati.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...