No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shettima ya wakilci shugaba Tinubu wajen jana’izar Sarkin Zuru

A ranar Juma’a Mataimakin Shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wajen jana’izar Sarkin Zuru, Manjo-Janar Muhammadu Sani Sami (ritaya), wanda aka yi a garin Zuru, Jihar Kebbi.

A wajen jana’izar, Shettima ya jaddada gagarumar gudummawar da marigayi Sarkin ya bayar, waɗanda ya ce ba za a taɓa mantawa da su ba.

KU KUMA KARANTA: Sarkin Zuru Muhammad Sami ya rasu a Landan

Ya ce, “Ana girmama sarakunan gargajiya a ƙasar mu saboda rawar da suke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya.”

Shettima ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa wajen jana’izar kuma ya isar da gaisuwar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ga gwamnatin Jihar Kebbi da iyalan marigayin da kuma dukkan al’ummar jihar.

Ɗimbim sarakuna, jami’an gwamnati, ‘yan kasuwa da sauran mutane sun halarci taron jana’izar.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...