No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sarkin Fika kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Yobe, Dokta Muhammadu Abali Ibn Muhammadu Idrissa, ya bayyana shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a matsayin abin da ke rura wutar rashin tsaro a jihar. 

Sarkin ya bayyana haka ne a lokacin wata liyafa da ya shirya ga ’yan jarida a fadarsa da ke ƙaramar hukumar Potiskum.

Ya ce harin baya-bayan nan da aka kai a yankin Gurjaje da ke ƙaramar hukumar Fika ta jihar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum daya tare da lalata gidaje sama da 100, ya tabbatar masa da alakar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da rashin tsaro.

KU KUMA KARANTA: An ba da umarnin ƙara tsaro a rumbunan NEMA don gudun masu warwason kayan abinci

Sarkin Fika ya buƙaci gwamnatin jihar da Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) ta fito da tsare-tsaren da za su dakile ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a jihar.

Ya kuma yi ƙira ga gwamnati da ta samar da cigaba a yankunan da lamarin ya shafa, yana mai kokawa kan taɓarɓarewar tattalin arziki a ƙasar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...