Connect with us

Labarai

SEMA ta ceto wani matashi a Yobe da ya yi yunƙurin kashe kansa, saboda ƙuncin rayuwa

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Yobe (YOSEMA) ta ceto wani matashi ɗan shekaru 30 da haihuwa (an sakaya sunansa) a Damaturu, babban birnin jihar daga yunƙurin kashe kansa saboda halin da ake ciki ƙuncin rayuwa.

A cewar shaidun gani da ido, wanda ya tsiran mazaunin gidajen Mai Mala, daura da Titin Gashuwa-Damaturu a Jihar Yobe wanda saboda takaici da matsin tattalin arziƙi da ya fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur da aka yi, ya yi yunƙurin kashe kansa ta hanyar shan gubar Ɓera.

Da lamarin ya faru, sai mutanen hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar (SEMA) suka bazama wurin da lamarin ya faru, inda suka garzaya da mutumin asibiti inda likitoci suka yi masa maganin kashe ƙwayoyin cuta, suka yi masa magani tare da yi wa wanda abin ya shafa nasiha.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun cafke mutumin da ya yi yunƙurin cinnawa masallaci wuta

An ruwaito cewa saƙon ya isa ga SEMA ta hannun ’yan banga na yankin da mahaifiyar matashin ta sanar da su. SEMA ta tabbatar da cewa wanda ya tsira yana karɓar magani.

Duk da haka, gwamnatin jihar ta hannun SEMA ta taimaka wa dangi da kayan abinci don rage illa da wahalhalu.

Da yake tabbatar da rahoton, babban sakataren ƙungiyar ta YOSEMA, Dakta Mohammed Goje ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.

“Eh gaskiya ne, amma nan da nan aka tura mazana zuwa wurin bayan da muka samu ƙiran gaggawa daga wasu nagartattun samari.

“A halin yanzu matashin yana karɓar magani.” Goje ya bayyana. Menene ra’ayinku game da waɗannan al’amura marasa kyau da cire tallafin man fetur ya haifar? ya tambaya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like