Connect with us

Labarai

Saudiyya ta soke bizar ’yan Najeriya 264 bayan saukarsu a Jidda

Published

on

Gwamnatin Saudiyya ta soke bizar ’yan Najeriya 264 da suka je Umrah a daidai lokacin da Shugaba Bola Tinubu ke ziyarar aiki a ƙasar.

Saudiyya ta soke bizar ɗaukacin ’yan Najeriya 264 da suka je ƙasar daga Kano da Legas ne, ta kuma ba da umarnin a dawo da su gida ne a ranar Lahadi.

Saukar jirgin kamfanin Air Peace da fasinjojin ke da wuya a Jiddah, jami’an filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz suka samu sanarwar cewa an soke bizar ɗaukacin fasinjojin da suka iso daga Najeriya.

Kafin barin Najeriya sai da aka yi wa fasinjojin tantacewa da binciken kwakwaf a filayen jirgi, da sanya idon hukumomin Saudiyya kuma aka tabbatar cewa bizarsu ba ta da matsala.

KU KUMA KARANTA: Za mu taimaka wa Najeriya ta gyara matatun manta – Saudiyya

Hakan ta faru ne a yayin da Shugaba Bola Tinubu da kusoshin gwamnatinsa suke halartar taron tattalin arzikin ƙasahen Larabawa da Afirka a Saudiyya, inda kuma suka yi Umrah.

Kimanin makonni biyu ke nan da Air Peace ya fara jigijalar fasinjoji kai-tsaye daga Najeriya zuwa Jidda.

“Muna zargin wannan wani shiri ne na sanya hakar fita a ran kamfanin, saboda akwai waɗanda ba su ji daɗin fara aikin Air Peace kai tsaye daga Najeriya zuwa Jidda ba, sabanin kamfanonin jiragen ƙasashen waje da suka fi shi tsada,” in ji wata majiya.

Aminiya ta gano daga bisani Ofishin Jakadancin Najeriya a Saudiyya ya rage adadin waɗanda za a dawo da su gida zuwa 177, waɗanda yawancinsu su tafi Saudiyya ne domin yin ibadar Umrah.

Kafin fara tashin Air Peace kai tsaye zuwa Jidda, kamfanin Saudiyya na yin wannan aiki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like