Sarkin Zuru Muhammad Sami ya rasu a Landan
Sarkin Zuru na Jihar Kebbi, ritaya Manjo-Janar Muhammadu Sani Sami, ya rasu yana da shekaru 81 a duniya
Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomi da Masarautu na Jihar Kebbi, Garba Umar-Dutsinmari, ne ya tabbatar da rasuwar mai martaba a cikin wata sanarwa da aka fitar a Birnin Kebbi ranar Lahadi.
KU KUMA KARANTA: Allah Ya yiwa mai martaba Sarkin Gudi Alhaji Isah Bunowo rasuwa
Ya bayyana cewa Sarkin ya rasu ne a daren Asabar a wani asibiti da ke birnin London bayan fama da jinya.









