No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga; Rabo Haladu.

MAJALISAR Dattawa ta amince da kudurin dokar kafa karin makarantun koyon aikin lauya a yankuna shidana kasar nan.

Majalisar ta amince da kudurin a zaman da ta yi yau Talata, 8 Fabrairu na 2022, bayan nazarin rahoton kwamitinta a kan harkokin shari’a da hakkin dan-Adam.

Makarantun da ake da su a yanzu su ne wadda take a Abuja; yankin arewa ta tsakiya, sai ta Kano, wadda ke Bagauda; yankin arewa maso yamma, sai ta Yola; yankin arewa maso gabas, sai ta Lagos; yankin kudu maso yamma da ta Enugu; yankin kudu maso gabas, da kuma ta Yenegoa a yankin kudu maso kudu.

Wadanda aka amince a kara sun hada da wadda za a yi a Kabba, Jihar Kogi a arewa ta tsakiya, da wata a Jos a yankin arewa maso tsakiyar ita ma, da ta Maiduguri a Jihar Borno domin arewa maso gabas, sai ta Argungu a Jihar Kebbi yankin arewa maso yamma.

Sauran su ne ta Okija a Jihar Anambra a yankin kudu maso gabas sai ta Orogun a Jihar Delta yankin kudu maso kudu, sai kuma ta Ilawe da ke Jihar Ekiti a kudu maso yamma.

admin
adminhttps://neptuneprimehausa.com
Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...