No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sace wayoyin da aka binne kusa da fadar shugaban ƙasa ya jefa unguwannin Abuja cikin duhu -TCN

Hukumar rarraba wutar lantarki ta Najeriya TCN tace wasu sun sace wayoyin layin rarraba wutar lantarkin karkashin kasa na 132kV dake baiwa tsakiyar Abuja da wasu unguwanni.

Mai magana da yawun hukumar ta TCN Ndidi Mbah ya fadi haka a wata takardar manema labarai da ya fitar yau Juma’a inda yace “a yankin gurin hutawa na Millenium Park da ke kusa da fadar shugaban kasa ta Aso Villa ne masu satar suka sace mita arba’in na abinda ke rarraba wuta na XLPE conductors.”

KU KUMA KARANTA:Hari kan layin wutar lantarki ya jefa Abuja cikin duhu

Ya kara da cewa wannan satar za ta haddasa rashin wuta a unguwannin Maitama, Wuse, Jabi, Life Camp, Asokoro, Utako da Mabushi.

Sanarwar tace tuni injiniyoyi na aiki don ganin an gyara tare da dawo da wutar a wadannan unguwanni da abin ya shafa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...