No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sabbin sarakunan Rano da Ƙaraye masu daraja ta biyu sun yi mubaya’a ga Sarki Sanusi

Daga Idris Umar, Zariya

Sabbin sarakunan Rano da Ƙaraye masu daraja ta biyu da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya naɗa a matsayin masu daraja ta biyu, sun yi mubaya’a ga Sarkin Kano na 16, Khalifa Muhammadu Sanusi II a ranar Laraba.

Sun kai wa sarki Sanusi II ziyarar ne sa’o’i kaɗan bayan Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana naɗin nasu.

Sabbin sarakunan sun haɗa da, Alhaji Muhammad Maharaz na Ƙaraye, Muhammad Isah Umar na Rano, da Alhaji Aliyu Abdulkadir na Gaya.

Sun yi mubaya’a ga Sarki Sanusi a zaman fadar da aka gudanar ranar Laraba.

Duk sarakunan biyu sun yi alƙawarin yin aiki a ƙarƙashin masarautar Kano mai daraja ta ɗaya tare da gode wa Gwamna Abba Yusuf bisa ganin sun cancanta har ya naɗa su .

KU KUMA KARANTA: Shekara ɗaya tayi wa Tinubu kaɗan ya warware matsalolin da ya gada – Sarki Sanusi

Idan za a iya tunawa, a ranar jiya talata 16 ga Yuli, 2024, Gwamnan ya rattaɓa hannu a kan dokar kafa masarautu masu daraja ta biyu a jihar.

Masarautar Rano da ta ƙunshi ƙananan hukumomin Rano, Kibiya, da Bunkure; sai masarautar Gaya da ta ƙunshi ƙananan hukumomin Gaya, Ajingi, da Albasu; ita kuma Ƙaraye ta ƙunshi ƙananan hukumomin Ƙaraye da Rogo.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...