No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf, ya buƙaci ɗan takarar gwamnan kano a jam’iyyar APC Nasiru Yusuf gawuna, yazo su haɗa kai domin ciyar da kano gaba.

Gwamnan ya buƙaci hakan ne, a yayin da yake jawabi ga manema labarai, jim kaɗan bayan futowa daga kotun ƙoli.

Abba yace, hukuncin kotun ƙolin ya kawo ƙarshen taƙaddamar da akeyi akan zaɓen daya gudana a ranar 18 ga watan Maris din shekarar data gabata.

KU KUMA KARANTA: Kotun ƙoli ta tabbatar da Abba Kabir Yusuf a matsayin halastaccen gwamnan Kano

Haka kuma gaskiya tayi halinta, duba da yadda kotun ƙoli ta tabbatar wa da Al’ummar kano abin da suka zaɓa.

Domin haka Abba yace ya kamata Gawuna yazo su haɗa kai, domin su kai kano matakin da zata zama abin kwaikwayo, a tsakanin ƙasashen duniya.

A ƙarshe zaɓaɓɓen gwamnan na kano yace, kofa a buɗe take ga dukkan ɓangaren ‘yan adawa domin suzo a ciyar da kano gaba, tunda dukkan su fatan da suke yi wa kano kenan.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...