No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rahotanni sun ce an lalata gidaje 15 da gonaki da dama sakamakon ruwan sama da ya yi ɓarna a unguwar Iyah Gbedde da ke ƙaramar hukumar Ijumu a jihar Kogi.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, lamarin da ya faru tsakanin Talata zuwa Alhamis, ya kuma bar zauren taron jama’a a ruguje.

Dakta Emmanuel Jeminiwa, shugaban ƙungiyar ci gaban Iyah Gbede na ƙasa, IDA, wanda ya zanta da manema labarai, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da takaici.

Mista Jeminiwa, wanda ya ƙasa bayar da adadin mutanen da abin ya shafa, ya bayyana cewa iyalai da dama sun zama marasa matsuguni da rashin taimako sakamakon lalata gidajensu.

KU KUMA KARANTA: Mutane sama da dubu biyu ne suka mutu a Libya, sakamakon ambaliyar ruwan sama

“Abin da ya fi damun mu shi ne noman abincinmu irin su dawa, rogo da masara da mamakon ruwan sama ya tafi da su wanda ya bar mu ba tare da wani zaɓi ba.

“Kun san cewa Iyah Gbede al’ummar noma ce, don haka ɓarnar amfanin gonakinmu. Har ila yau, bala’in ya shafi hanyoyin garinmu na al’umma kuma ya sa ba a iya wuce wa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa manoman da suke so su je su kwaso ragowar gonakin da abin ya shafa, ba za su iya zuwa ba saboda an lalata gadar da ke kan gonakin su ma.

Ya ce mutanen na matuƙar buƙatar taimako, inda ya ce ɓarnar da aka yi ya zarce abin da al’umma za su iya ɗauka.

Shugaban ya kuma yi ƙira ga Gwamnatin Tarayya da ta Jihohi da su taimaka wa al’umma domin da yawa daga cikin waɗanda abin ya shafa na tsugunne da abokai ko ‘yan uwa domin samun sauƙi.

Ya kuma yi ƙira ga Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa, (NEMA), Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha, (SEMA), ƙungiyoyin kamfanoni da masu hannu da shuni da su ceto al’umma. A halin da ake ciki, kwamishinan muhalli na jihar, Victor Omofeye, ya ce gwamnati na sane da lamarin.

Ya ce rahoton aukuwar lamarin ya isa ofishin sa kuma ana shirye-shiryen da ya kamata domin tantance irin ɓarnar da aka yi da kuma ganin yadda za a taimaka wa waɗanda abin ya shafa kamar yadda ake tsammani.

Kwamishinan ya gargaɗi mazauna jihar da su yi taka-tsan-tsan kuma ka da su zauna a kusa da wuraren da ambaliyar ruwa ta shafa domin ka da abin ya shafa bisa la’akari da gargaɗin da NiMET ta yi kan yadda ruwan sama ya yi ƙamari a bana da kuma illar da ke haifar wa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...