Rushewar gini a Jigawa mutum 1 ya mutu, 7 sun jikkata

0
131
Rushewar gini a Jigawa mutum 1 ya mutu, 7 sun jikkata

Rushewar gini a Jigawa mutum 1 ya mutu, 7 sun jikkata

Daga Jameel Lawan Yakasai

Mutum ɗaya ya rasu yayin da wasu bakwai suka jikkata a rugujewar wani gini da ruwan sama ya haddasa a ƙauyen Kabak, karamar hukumar Kirikasamma, jihar Jigawa.

Jami’in yaɗa labarai na karamar hukumar, Musa Muhammad, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce mutum biyar aka kwantar a asibiti yayin da aka sallami biyu bayan samun magani.

KU KUMA KARANTA: Mutum 3 sun mutu a Legas bayan rushewar gini

Shugaban karamar hukumar, Muhammad Maji, ya ziyarci wurin tare da bayar da tallafin kuɗi domin kula da wadanda suka jikkata da kuma iyalan da suka rasa ɗan uwansu.

Lamarin ya zo ne a daidai lokacin da ake cigaba da fuskantar matsalar rushewar gine-gine a sassa daban-daban na ƙasar, musamman a biranen Abuja da Lagos.

Leave a Reply