'Yansanda
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama mutane 49 da ake zargi da sata a Triumph Plaza Kano
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/06/IMG-20230605-WA0007.jpg)
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama mutane 49 da ake zargi da sata a shagunan kasuwanci dake Triumph a ƙaramar Hukumar Fagge dake jihar Kano.
Hakan na ɗauke cikin wata sanarwar manema labarai da Kakakin Rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Litinin.
KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutane biyu da laifin daɓa wa matashi wuƙa, ya mutu har lahira
“A ranar Lahadin da ta gabata da misalin ƙarfe 10 na dare, rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta samu rahoton cewa wasu ɓata gari sun yi ayari sun nufi unguwar Fagge dan yin satar kayayyakin mutane a Triumph Plaza.” Inji Sanarwar.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/06/IMG-20230605-WA0008.jpg)
“Da samun wannan rahoto kwamishinan ‘yan Sanda CP Mohammed Usaini Gumel ya bada umarni ga dakarun ‘yan sanda na Operation ‘Restore Peace’ inda suka yi nasarar fatattakar ɓarayin. An kuma yi nasarar kama 49 daga cikin su tare da ceto wasu kayayyaki da suka sata.”
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/06/IMG-20230605-WA0005.jpg)
“Daga kayan da aka yi nasarar ceto wa, akwai ƙofofin alfarma guda 3, tagogi, Na’urar sanyaya ɗaki guda 4, ƙarafunan ƙofa guda 8, da kuma manyan guduma ta fasa gini guda 16.” Inji sanarwar
Rundunar tace ana ci gaba da gudanar da bincike, ta kuma ja hankalin iyaye da jagororin al’umma da su tsawatarwa yaran su da gujewa satar kayan mutane.
A kwanakin nan an samu yawaitar satar kayan mutane a wuraren da gwamnatin Jihar Kano ta yi rusau inda matasan ke iƙirarin ganima suke ɗiba.
'Yansanda
An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci
![An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/2c27c23e2a85f90c.jpg)
An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci
Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.
Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.
A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.
Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.
KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe
Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.
Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.
Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.
'Yansanda
‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara
![Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG-20240628-WA0262.jpg)
‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara
Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.
Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”
Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.
Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.
Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.
KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara
Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.
“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.
“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.
“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.
“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.
“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.
“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.
'Yansanda
‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga
!['Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/Police-1.jpg)
‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga
Daga Muhammad Kukuri
Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.
’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.
An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.
Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.
Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.
KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu
“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.
“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.
Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: ‘Yan sanda sun kama ɗan fursunan da ya tsere daga gidan yarin Owerri a Ribas | Neptune Prime Hausa