No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dubun wasu matasa uku da rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama da wayoyin hannu 318 waɗanda ake zargin na sata ne ta cika.

Kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana haka a wani saƙo da ya wallafa a shafin sada zumunta ranar Asabar.

Kiyawa ya bayyana cewa tun da farko wani mai suna Muhammad Adam da wasu mutane 9 ne suka kai musu ƙorafi kan cewa da tsakar dare ɓarayi sun fasa musu shaguna a kusa da filin wasa na Sani Abacha dake ƙofar Mata Kano, inda suka sace wayoyi 671.

Nan take ‘yan sanda suka soma bincike wanda har ya kai ga kama mutanen uku, sun kuma amsa laifin da ake zargin su da aikata wa.

KU KUMA KARANTA: An kama ɓarayin da suka fasa shago suka saci wayoyin hannu 996 da kwamfuta tara

Sai dai waɗanda ake zargin sun shaida wa ‘yan sandan cewa tuni suka sayar da wasu daga cikin wayoyin.

SP Kiyawa ya bayyana cewa za a gurfanar da mutunen a gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...