Rundunar sojojin ruwan Najeriya ta bankaɗo wata runduna ta bogi da ke yi mata Sojan Gona

Hedikwatar rundunar mayaƙan ruwan Najeriya ta gano masu yi mata sojan gona a matsayin sojojin ruwa.

Kakakin mayaƙan ruwan Najeriya, Navy Commodore Ayo Vaughan ya shaida wa VOA Hausa cewa su waɗannan sojojin ruwan bogi da aka gano na da hedikwatarsu a shiyyar kudu maso kudancin Najeriya ne, inda suke gudanar da haramtacciyar hada-hadarsu.

Za ka gansu tsaf-tsaf cikin kakin sojojin ruwa maƙale da lambobin girma da ababen dai da ke jikin kakin sojin ruwan har ma wani babban ofis suke da shi da adireshin yanar gizo, har ma sai da form na ɗaukar aiki su ke yi inda suke damfarar jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya sun sake ceto ɗaya daga cikin ‘yan matan Chiɓok

Wannan rundunar mayaƙan na bogi na nuna izza da isa yayin da a wani lokaci suke cin zalin jama’a a matsayin su sojoji ne.

Saboda haka Hedikwatar mayaƙan Ruwan Najeriya ta ce za ta ɗau mataki mai tsanani akansu kana ta nemi jama’a da su yi taka tsantsan, sannan su kai rahoton duk waɗanda ba su yarda da take-takensu ba.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *