No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar sojojin ƙasa ta Najeriya ta fitar da hotunan wasu mutane da take nema ruwa-a-jallo bisa zargin kisan dakarunta goma sha bakwai a jihar Delta da ke kudancin ƙasar.

Rundunar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, kwana guda bayan an yi wa sojojin jana’izar ban-girma a Abuja, babban birnin ƙasar.

Mutanen takwas, ciki har da mace, su ne Akevwru Daniel Omotegbono wanda aka fi sani da suna Amagbem; Prof. Ekpekpo Arthur, Andaowei Dennis Bakriri da Igoli Ebi.

KU KUMA KARANTA: Dakarunmu ba za su bar yankin Neja-Delta ba har sai an kamo waɗanda suka aikata kisan gillar – Rundunar Soji

Sauran su ne Akata Malawa David, Sinclair Oliki, Clement Ikolo Oghenerukevwe da kuma Reuben Baru.

Kusan mako biyu kenan Shugaba Tinubu ya bai wa hedkwatar tsaro da shugaban rundunar tsaron Najeriya “cikakken iko” na hukunta duk wanda aka samu da laifin kisan sojojin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...