No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rikicin ruwa yana haifar da rikice-rikice a duniya – Shugaba Erdogan

Shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdoğan ya yi kira da a mayar da hankali kan yadda rikicin ruwa ke ƙara taɓarɓarewa a duniya.

“Yawancin rikice-rikice a Asiya da Amurka da Arewacin Afirka, da kuma Gabas ta Tsakiya sun samo asali ne daga taƙaddamar hanyoyin ruwa,” in ji Erdogan a ranar Juma’a a jawabin da ya yi a wani taron albarkatun noma da Bankin Ziraat na kasar Turkiyya ya shirya a Istanbul.

Ya ƙara da cewa, “Sakamakon illar da sauyin yanayi ke haifarwa, hanyoyin ruwa da wuraren da tafkuna suke suna zama wuraren da ake fama da rikici.”

KU KUMA KARANTA: Turkiyya ce ta aika da kayan agaji  mafi yawa zuwa Gaza da ya kai tan 50,000 — Erdogan

Erdogan ya kuma taɓo batun cinikin hatsin da Turkiyya da Majalisar Dinkin Duniya suka ƙulla tsakanin Rasha da Ukraine a shekarar 2022.

“Idan ba don yarjejeniyar cinikin hatsin da Turkiyya ke jagoranta ba, da da yawa yankunan sun yi fama da yunwa musamman ƙasashen Afirka,” in ji shi.

Shugaban ya jaddada cewa Turkiyya “ta hana lamarin yin muni ta hanyar tabbatar da wucewar tan miliyan 33 na hatsi ta cikin mawuyacin hali” a cikin bala’in cutar ta Covid-19 da yakin Ukraine.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...