No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani sabon rikici a kan jayayyar filaye ya sake ɓarkewa a tsakanin al’ummomin garuruwan Ilobu da Ifon da ke maƙwabtaka da juna a Jihar Osun.

An fara rikicin ne cikin daren Laraba zuwa wayewar garin Alhamis.

Wata majiya ta ce mutum ɗaya ya rasa ransa a wajen rikicin sannan an yi ƙone-ƙonen gidaje da kadarori kafin gamayyar jami’an tsaro su shawo kan lamarin.

Wasu majiyoyi a yankin sun shaida wa Aminiya cewa an ga ɗimbin mutane maza da mata suna ƙoƙarin ƙauracewa garuruwan.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Bauchi za ta sasanta rikicin kan iyaka da Jigawa

Da take tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Laraba, Kakakin Rundunar ’Yan Sanda a Jihar, Yemisi Opalola ta ce an yi wa jami’an ’yan sandan da aka tura su kwantar da rikicin kwanton ɓauna da aka harbi babban jami’i (DPO) da jami’ansa 4 tare da ƙona sabuwar motar sintiri a lokacin rikicin.

Kakakin ’yan sandan ta ce duk da yake an shawo kan lamarin sai dai har zuwa lokacin rubuta wannan labari waɗannan jami’an ’yan sanda suna kwance a asibiti da likitoci suke ƙoƙarin ceton rayukansu.

A wani labarin kuma, Gwamnan Jihar, Ademola Adeleke, ya ba jami’an tsaro umarnin harbin duk wanda aka gani yana ƙoƙarin sake tayar da rikici a yankunan.

Gwamnan ya kuma tunatar da mazauna yankin cewa dokar hana fitar da ya sanya har yanzu tana nan daram.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...