No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙasar Rasha ta gudanar da atisayen soji domin tabbatar da cewa tana cikin shirin iya kai gagarumin farmakin nukiliya a cewar ministan tsaron ƙasar, Sergei Shoigu.

Atisayen ya haɗa da “martani kan harin makamin nukiliya daga maƙiya”, in ji ministan tsaron.

Kafar talabijin ta ƙasar ta nuno ministan yana yi wa shugaba Putin bayani kan atisayen.

Lamarin ya zo ne daidai lokacin da majalisar dokokin ƙasar Rasha ta goyi bayan janyewar da ƙasar ta yi daga yarjejeniyar ƙasa da ƙasa kan haramta gwajin makaman nukiliya.

KU KUMA KARANTA: Rasha ta harbo jiragen Yukiren marasa matuƙa 31 a yankunan kan iyaka

Rasha da Amurka sukan yi atisayin gwajin makamin nukiliya a kai-a kai, inda Rasha ta saba yin nata a ƙarshen watan Oktoba.

Sanarwar da Kremlin ta fitar ta ce atisayen na baya-bayan nan sun haɗa da harba nau’uka daban-daban na muggan makamai masu linzami, waɗanda suka haɗa da makami mai linzami da ake iya amfani da shi wajen kai hari tsakanin nahiyoyi da makami mai linzami da aka harba daga wani jirgin ruwa mai ƙarfin nukiliya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...