No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙasar Rasha ta sake buɗe ofishin jakadancinta a Burkina Faso a ranar Alhamis bayan shafe kusan shekaru 32, a cewar sanarwar gwamnatin ƙasar da ke yankin Afirka ta Yamma da kuma jami’in diflomasiyyar Rasha suka fitar.

An rufe ofishin ne a shekarar 1992, a cewar Jakadan Rasha a makwabciyar kasar Ivory Coast Alexei Saltykov, shugaban Rasha Vladimir Putin zai nada sabon jakadan Rasha a Burkina Faso.

A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Burkina Faso ta fitar ta tabbatar da cewa “Rasha ta sake buɗe ofishin jakadancinta a yau Alhamis a Ouagadougou.”

Saltykov ya ce zai jagoranci ayyukan diflomasiyyar Rasha a Burkina Faso har sai an nada sabon jakadan, yana mai bayyana Burkina Faso a matsayin “tsohuwar abokiyar hulda da muke da kyakkyawar alaƙa ta abota.”

KU KUMA KARANTA: Yukiren ta ce ta kakkaɓo jirage marasa matuƙi na Rasha sama da 70

A bara Burkina Faso ta fuskanci juyin mulkin soji har sau biyu — sun samo asali ne sakamakon rashin gamsuwa da kuma gazawar da aka yi wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro ta masu tada ƙayar baya.

Tun bayan hawan su mulki a watan Satumban 2022, gwamnatin mulkin sojin kasar ta nesanta kanta daga Faransa, daɗaɗɗiyar abokiyar huldarta, sannan wacce ta mata mulkin mallaka, kana ta matsa kusa da Rasha.

A watan Oktoba ne Burkina Faso ta ƙulla yarjejeniya da ƙasar Rasha kan gina tashar makamashin nukiliya domin ƙara samar da makamashi a yankin Sahel inda ƙasa da kashi ɗaya cikin huɗu na al’ummar ƙasar ke samun wutar lantarki.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...