No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Kotun ɗaukaka ƙara dake zaman ta a sakatariyar Audu Baƙo a Kano, ta ɗage ci gaba da sauraren shari’ar da Abduljabbar Nasir Kabara, ya ɗaukaka kan hukuncin kisa ta hanyar rataya, da babbar kotun shari’ar addinin musulunci dake zaman ta a Ƙofar Kudu, ta yanke masa bisa zarginsa da laifin yin ɓatanci ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad S.A.W.

Kotun ɗaukaka ƙarar ƙarƙashin jagorancin, Justice Nasiru Yusuf da kuma A’isha Mahmud , sun saurari ƙarar a ranar Litinin ɗin nan.

Lauyan Abduljabbar Nasiru Kabar, Barista Yusuf Sadik, ya shaida wa kotun cewar a shirye suke don ci gaba da sauraren shari’ar.

KU KUMA KARANTA: Yadda ta kasance a babbar kotun Kano kan sauraren ƙarar da Mal. Abduljabbar ya shigar

Sai dai lauyan gwamnatin Kano Barista Bashir Saleh, ya roƙi kotun da ta ƙara musu lokaci kafin a ci gaba da sauraren shari’ar.

Lauyan Abduljabbar Nasiru Kabara, ya nuna rashin jin daɗinsa, sakamakon yace tun tuni ya sada lauyan gwamnatin da takaddun martaninsu tun a watan Fabarairun 2024, inda ya nemi gwamnatin Kano ta biyashi naira miliyan 20, sakamakon ɓata masa lokaci da aka yi.

Alƙalan kotun, Justice Nasiru Saminu da Justice A’isha Mahmud, sun bincika takardun da lauyan Abduljabbar Nasiru Kabara, ya yi iƙirarin ya sadar da lauyan gwamnatin Kano, inda aka gano cewar a watan Maris ya ba wa lauyan gwamnatin takardun martanin .

Daga bisani lauyan Abduljabbar Nasiru Kabara, ya janye buƙatar Neman Gwamnatin ta biya shi naira miliyan 20.

Alƙalan kotun ɗaukaka ƙarar sun ɗage ci gaba da sauraren shari’ar, zuwa ranar 9 ga watan Mayun 2024, don ci gaba da sauraren shari’ar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...