'Yansanda
PSC ta amince da korar jami’an ‘yan sanda 3, ta kuma rage ma’aikata 5 daga aiki
Hukumar da ke kula da aikin ‘yan sanda, PSC, ta amince da korar jami’an ‘yan sanda uku tare da rage masu muƙami biyar.
Shugaban ‘yan jarida da hulɗa da jama’a na PSC Ikechukwu Ani ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba a Abuja, inda ya ce an tsawatar da wasu jami’ai 20 da su ka mutu.
Ya ce jami’an da aka kora sun haɗa da mataimakan sufiritandan ‘yan sanda uku, yayin da waɗanda rage ma’aikata ya shafa sun haɗa da mataimakin kwamishina, babban sufeton ‘yan sanda, sufeto biyu da mataimakin sufeto ɗaya.
Mista Ani ya ce waɗanda aka yiwa tsawatar mai tsanani sun haɗa da mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, babban sufeton ‘yan sanda, sufiritanda huɗu, mataimakan sufiritanda biyu da mataimakan sufiritanda 12.
KU KUMA KARANTA: Rundunar ’yan sanda ta ba da miliyan 18 ga iyalan jami’anta da suka mutu
Ya ce an yanke shawarar ne a yayin babban taron hukumar karo na 20, wanda shugaban hukumar Dakta Solomon Arase ya jagoranta.
Mista Ani ya ce taron ya yi la’akari da batutuwa 43 na ladabtarwa, ɗaukaka ƙara da kuma ƙararraki. Kakakin hukumar ta PSC ya ce shugaban hukumar ya yi alƙawarin ba da fifiko kan jindaɗin jami’an ‘yan sanda sosai a kan laifukan cin zarafi idan ya cancanta.
Ya ce taron ya kuma amince da tsawatarwa na jami’ai shida, Sufeto ɗaya da mataimakan Sufiritanda biyar. Mista Ani ya ƙara da cewa an amince da ƙarin girma ga manyan ma’aikatan hukumar 109 a yayin taron.
'Yansanda
An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci
An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci
Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.
Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.
A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.
Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.
KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe
Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.
Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.
Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.
'Yansanda
‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara
‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara
Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.
Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”
Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.
Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.
Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.
KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara
Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.
“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.
“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.
“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.
“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.
“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.
“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.
'Yansanda
‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga
‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga
Daga Muhammad Kukuri
Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.
’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.
An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.
Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.
Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.
KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu
“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.
“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.
Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: ‘Yan sanda sun kwato bindigogi ƙirar AK-47 guda huɗu a Kano | Neptune Prime Hausa
Pingback: Kwamishinan ‘yan sandan Kwara ya ba da umarnin kama jami’in da ya bugu a cikin faifayin bidiyo | Neptune Prime Hausa
Pingback: Hukumar ‘yan sanda ba za ta amince da cin zarafin jami’anta ba – Arase | Neptune Prime Hausa
Pingback: Hukumar kula da aikin ‘yan Sanda ta amince da biyan albashin ma’aikatan 2021/2022 | Neptune Prime Hausa