Connect with us

Ƙasashen Waje

Paul Alexander, majinyacin da ke numfashi da huhun ƙarfe ya mutu

Published

on

Paul Alexander ya rasu ranar Litinin yana da shekaru 78, a cewar wata sanarwa da ɗan’uwansa, Philip Alexander, ya fitar ta kafar sada zumunta.

Paul Alexander, wanda ya mutu yana da shekaru 78 a duniya ya kamu da cutar shan inna yana da shekaru 6, ya kuma rayu na tsawon shekaru 70 yana numfashi ta wajen amfani da injin numfashi. Duk da haka, ya samu damar samun digiri na shari’a, ya kuma rubuta littafi.

Bayan da cutar shan inna ta shanye shi yana a shekara 6, lamarin ya tilastawa Paul Alexander dogara ga amfani da huhun ƙarfe.

Rayuwa a cikin huhun ƙarfe sakamakon kamuwa da cutar shan inna bai hana Alexander zuwa jami’a ba, ya samu digiri na shari’a da kuma aikin lauya fiye da shekaru 30 da suka shige. Lokacin da yake yaro, ya koya wa kansa numfashi na tsawon mintuna da sa’o’i a lokaci guda, duk da haka ya zama dole ya yi amfani da injin a kowace rana ta rayuwarsa.

Ya kasance ɗaya daga cikin mutane kaɗan da su ka rage a Amurka da ke zaune a cikin huhun ƙarfe. Kuma a cikin makonnin ƙarshe na rayuwarsa, ya nuna wa mabiyansa na TikTok yadda ya ke rayuwarsa da taimakon injin.

Ba a bayyana dalilin mutuwarsa a hukumance ba. Amma Alexander ya ɗan jima yana asibiti don ya kamu da cutar Covid-19 a watan Fabrairu, a cewar shafinsa na TikTok. Bayan ya koma gida, Alexander ya yi fama da rashin cin abinci da shan ruwa yayin da yake murmurewa daga cutar, wacce ke auka wa huhu kuma tana iya zama haɗari musamman ga mutanen da suka tsufa kuma suna da matsalar numfashi.

Alexander ya kamu da cutar shan inna a shekara ta 1952, a cewar littafinsa, “Three Minutes for a Dog: My Life in an Iron Lung.” wanda ya rubuta ta hanyar sanya Alƙalami ko fensir a bakinsa. Nan take likitocin asibitin Parkland da ke Dallas suka sanya shi cikin huhun ƙarfe domin ya samu yin numfashi.

Lokacin da yake cikin injin, Alexander yakan buƙaci taimakon wasu don ayyuka na yau da kullum kamar ci da sha.

KU KUMA KARANTA:Hukumar kwastom ta kama muggan ƙwayoyi da makamai a tashar jiragen ruwa na Legas

Alexander ya ƙaddamar da shafin TikTok ɗinsa a watan Janairu, kuma, tare da taimakon wasu, ya fara ƙirƙirar bidiyo game da rayuwarsa.

A cikin wani bidiyo, Alexander yayi cikakken bayani game da ƙalubalen tunani na rayuwa a cikin huhun ƙarfe.

“Akwai kaɗaici,” in ji shi “Wani lokaci ina cikin matsananciyar damuwa saboda ba zan ma iya taɓa wani ba, hannayena ba sa motsowa.”

Alexander ya faɗa a cikin bidiyon cewa ya shafe shekaru da dama yana samun saƙonnin imel da wasiƙu daga mutanen da ke fama da damuwa da kaɗaici, ya kuma ba su shawarwari.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Published

on

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Daga Ibraheem El-Tafseer

Me magana da yawun Shelkwatar zaɓe ta Iran Dakta Muhsin Elsami, ya sanar da cewa, an kammala lissafi ƙuri’a Miliyan 25 na zaɓen shugaban ƙasar Iran wanda aka fara ranar juma’a.

‘Yan takara 6 ne suka tsallake matakin ƙarshe yayin da 2 suka fice saboda ra’ayin kai, ana zaɓe saura kwana 2.

Dakta Mas’ud Pezeshkian shi ne kan gaba da ƙuri’a Miliyan 10.415.991

Dakta Sa’ed Jalili ya samu ƙuri’u Miliyan 9.473298

Se kuma Dakta Qalibaf ya samu ƙuri’a Miliyan 3.383.340

Sai Ayatullah Musfata ya samu ƙuri’a 206.397.

Yanzu haka an fitar da Dakta Baqir Qalibaf da Ayatullah Musfata da suke da ƙarancin ƙuri’a, ya rage saura Dakta Jalili da Dakta Mas’ud Pezeshkian da ken gaba.

KU KUMA KARANTA: Iran ta tabbatar da mutuwar shugaban ƙasar, Ebrahim Ra’isi, a hatsarin jirgin sama

Jami’i Muhsin Elsami ya sanar da cewa za’a shiga matakin zaɓe na 2 ranar Juma’a mai zuwa inda za a kara tsakanin Dakta Jalili da Dakta Mas’ud.

Cikin su duk wanda ya samu kaso 50 ya zama shugaban ƙasar Iran, wanda zai maye gurbin Shahid Ebrahim Ra’isi wanda ya rasu sanadiyyar hatsarin jirgin Helikofta, a watan da ya gabata.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra’ila kan Shugaba Erdogan

Published

on

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra'ila kan Shugaba Erdogan

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra’ila kan Shugaba Erdogan

Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta yi Allah wadai da wani saƙo da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila, Israel Katz ya wallafa a shafukan sada zumunta a baya-bayan nan kan shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, inda ta bayyana hakan a matsayin wani yunƙuri na Isra’ila na ɓoye laifukanta.

Sanarwar da Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta fitar a ranar Talata ta ce “Muna daukar wannan matsayi na rashin mutuntawa da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila ke yi wa mai girma shugaban kasarmu a matsayin wani lamari da za a ji shi ne kawai daga bakin ƙasar da ake zarginta da kisan kiyashi.”

Yayin da take suka da kakkausar murya a shafukan sada zumunta, ma’aikatar ta ce: “Irin wannan ƙazafi da ƙarya wani ɓangare ne na ƙoƙarin Isra’ila na ɓoye laifukan da ta aikata.”

Turkiyya ta ƙara da cewa, za ta ci gaba da fafutukar tabbatar da zaman lafiya da adalci.

KU KUMA KARANTA: Ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza – Ministan Turkiyya

Isra’ila, wadda ta yi fatali da ƙudurin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ke neman tsagaita wuta cikin gaggawa, ta fuskanci tofin Allah-tsine a tsakanin kasashen duniya a ci gaba da kai munanan hare-hare kan Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Fiye da Falasɗinawa 37,700 aka kashe tun daga lokacin a Gaza, yawancinsu mata da yara, kuma kusan wasu 86,400 sun jikkata, a cewar hukumomin lafiya na yankin.

Sama da watanni takwas da yakin Isra’ila a Gaza, inda yankuna da dama suka zama kufai a cikin yankin da aka yi wa ƙawanya da hana shigar da abinci da ruwan sha da magunguna.

Ana tuhumar Isra’ila da aikata kisan kiyashi a Kotun Duniya, wanda hukuncin na baya-bayan nan ya umarci Tel Aviv da ta dakatar da kai hare-hare a kudancin birnin Rafah, inda Falasɗinawa sama da miliyan guda suka nemi mafaka daga yakin kafin a mamaye shi a ranar 6 ga watan Mayu.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like