Connect with us

Ƙasashen Waje

Paul Alexander, majinyacin da ke numfashi da huhun ƙarfe ya mutu

Published

on

Paul Alexander ya rasu ranar Litinin yana da shekaru 78, a cewar wata sanarwa da ɗan’uwansa, Philip Alexander, ya fitar ta kafar sada zumunta.

Paul Alexander, wanda ya mutu yana da shekaru 78 a duniya ya kamu da cutar shan inna yana da shekaru 6, ya kuma rayu na tsawon shekaru 70 yana numfashi ta wajen amfani da injin numfashi. Duk da haka, ya samu damar samun digiri na shari’a, ya kuma rubuta littafi.

Bayan da cutar shan inna ta shanye shi yana a shekara 6, lamarin ya tilastawa Paul Alexander dogara ga amfani da huhun ƙarfe.

Rayuwa a cikin huhun ƙarfe sakamakon kamuwa da cutar shan inna bai hana Alexander zuwa jami’a ba, ya samu digiri na shari’a da kuma aikin lauya fiye da shekaru 30 da suka shige. Lokacin da yake yaro, ya koya wa kansa numfashi na tsawon mintuna da sa’o’i a lokaci guda, duk da haka ya zama dole ya yi amfani da injin a kowace rana ta rayuwarsa.

Ya kasance ɗaya daga cikin mutane kaɗan da su ka rage a Amurka da ke zaune a cikin huhun ƙarfe. Kuma a cikin makonnin ƙarshe na rayuwarsa, ya nuna wa mabiyansa na TikTok yadda ya ke rayuwarsa da taimakon injin.

Ba a bayyana dalilin mutuwarsa a hukumance ba. Amma Alexander ya ɗan jima yana asibiti don ya kamu da cutar Covid-19 a watan Fabrairu, a cewar shafinsa na TikTok. Bayan ya koma gida, Alexander ya yi fama da rashin cin abinci da shan ruwa yayin da yake murmurewa daga cutar, wacce ke auka wa huhu kuma tana iya zama haɗari musamman ga mutanen da suka tsufa kuma suna da matsalar numfashi.

Alexander ya kamu da cutar shan inna a shekara ta 1952, a cewar littafinsa, “Three Minutes for a Dog: My Life in an Iron Lung.” wanda ya rubuta ta hanyar sanya Alƙalami ko fensir a bakinsa. Nan take likitocin asibitin Parkland da ke Dallas suka sanya shi cikin huhun ƙarfe domin ya samu yin numfashi.

Lokacin da yake cikin injin, Alexander yakan buƙaci taimakon wasu don ayyuka na yau da kullum kamar ci da sha.

KU KUMA KARANTA:Hukumar kwastom ta kama muggan ƙwayoyi da makamai a tashar jiragen ruwa na Legas

Alexander ya ƙaddamar da shafin TikTok ɗinsa a watan Janairu, kuma, tare da taimakon wasu, ya fara ƙirƙirar bidiyo game da rayuwarsa.

A cikin wani bidiyo, Alexander yayi cikakken bayani game da ƙalubalen tunani na rayuwa a cikin huhun ƙarfe.

“Akwai kaɗaici,” in ji shi “Wani lokaci ina cikin matsananciyar damuwa saboda ba zan ma iya taɓa wani ba, hannayena ba sa motsowa.”

Alexander ya faɗa a cikin bidiyon cewa ya shafe shekaru da dama yana samun saƙonnin imel da wasiƙu daga mutanen da ke fama da damuwa da kaɗaici, ya kuma ba su shawarwari.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra’ila kan Shugaba Erdogan

Published

on

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra'ila kan Shugaba Erdogan

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra’ila kan Shugaba Erdogan

Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta yi Allah wadai da wani saƙo da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila, Israel Katz ya wallafa a shafukan sada zumunta a baya-bayan nan kan shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, inda ta bayyana hakan a matsayin wani yunƙuri na Isra’ila na ɓoye laifukanta.

Sanarwar da Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta fitar a ranar Talata ta ce “Muna daukar wannan matsayi na rashin mutuntawa da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila ke yi wa mai girma shugaban kasarmu a matsayin wani lamari da za a ji shi ne kawai daga bakin ƙasar da ake zarginta da kisan kiyashi.”

Yayin da take suka da kakkausar murya a shafukan sada zumunta, ma’aikatar ta ce: “Irin wannan ƙazafi da ƙarya wani ɓangare ne na ƙoƙarin Isra’ila na ɓoye laifukan da ta aikata.”

Turkiyya ta ƙara da cewa, za ta ci gaba da fafutukar tabbatar da zaman lafiya da adalci.

KU KUMA KARANTA: Ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza – Ministan Turkiyya

Isra’ila, wadda ta yi fatali da ƙudurin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ke neman tsagaita wuta cikin gaggawa, ta fuskanci tofin Allah-tsine a tsakanin kasashen duniya a ci gaba da kai munanan hare-hare kan Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Fiye da Falasɗinawa 37,700 aka kashe tun daga lokacin a Gaza, yawancinsu mata da yara, kuma kusan wasu 86,400 sun jikkata, a cewar hukumomin lafiya na yankin.

Sama da watanni takwas da yakin Isra’ila a Gaza, inda yankuna da dama suka zama kufai a cikin yankin da aka yi wa ƙawanya da hana shigar da abinci da ruwan sha da magunguna.

Ana tuhumar Isra’ila da aikata kisan kiyashi a Kotun Duniya, wanda hukuncin na baya-bayan nan ya umarci Tel Aviv da ta dakatar da kai hare-hare a kudancin birnin Rafah, inda Falasɗinawa sama da miliyan guda suka nemi mafaka daga yakin kafin a mamaye shi a ranar 6 ga watan Mayu.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Shugaba Ruto na Kenya ‘ba zai’ sa hannu a kan sabuwar dokar ƙarin haraji ba

Published

on

Shugaba Ruto na Kenya 'ba zai' sa hannu a kan sabuwar dokar ƙarin haraji ba

Shugaba Ruto na Kenya ‘ba zai’ sa hannu a kan sabuwar dokar ƙarin haraji ba

Shugaban Kenya, William Ruto ya ce ba zai rattaba hannu kan wata doka mai cike da cece-kuce da ta haifar da zanga-zanga a faɗin ƙasar ba, har aka harbe mutane da dama.

Masu zanga-zangar sun mamaye majalisar ne bayan da ‘yan majalisar suka zartar da dokar a ranar Talata. Kudirin zai kara yawan haraji da kuma tsadar rayuwa.

“Bayan yin la’akari da ci gaba da tattaunawa game da abubuwan da ke ƙunshe a cikin kudirin kudi na 2024, da kuma sauraron jama’ar Kenya, wadanda suka yi kira da babbar murya cewa ba sa son wani abu da wannan ƙudirin kuɗi na 2024, na yarda, don haka ba zan sanya hannu ka dokar ba, kuma daga baya za a janye shi,” Ruto ya shaida wa taron manema labarai a fadar gwamnati da ke Nairobi babban birnin ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

“Mutane sun rasa rayukansu kuma abin takaici ne matuka, da ma hakan bai faru ba,” ya ƙara da cewa.

Zanga-zangar ta jawo gwamnati ta girke sojoji don shawo kan karya doka da oda.
Sai dai wata Babbar Kotu ta soke umarnin girke sojojin.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Published

on

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Ƙungiyar likitoci ta Kenya ta ce adadin waɗanda suka mutu, sanadiyar zanga-zangar ƙarin kuɗin haraji da gwamnatin ƙasar ta sanar, ya ƙaru zuwa 13.

Shugaban Ƙungiyar Simon Kigondu ne ya tabbatarwa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP adadin, a wata zantawa da suka yi da shi a yau Laraba.

Masu zanga-zangar waɗanda yawancinsu matasa ne, sun mamaye zauren majalisar dokokin kasar a jiya Talata, inda suka rinka jifar ‘yan sanda da duwatsu da kuma rushe shingen jami’an tsaro don kutsa kai cikin harabar majalisar.

Bayan faruwar lamarin, shugaban ƙasar William Ruto ya tura da jami’an soji don tarwatsa masu zanga-zangar.

KU KUMA KARANTA: Mutum 12 sun mutu a rikicin da ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasa a Chadi

Shugaba Ruto ya lashi takobin ɗaukar tsauraran matakai don tabbatar da zaman lafiya a ƙasar, inda ya sha alwashin hukunta wadanda ke da hannu a lamarin.

Sai dai duk da ɗaukar wancan mataki, masu zanga-zangar sun ce babu gudu babu ja da baya game da ƙudirinsu na ci gaba da zanga-zangar, har sai haƙarsu ta cimma ruwa.

Wani jami’i a asibitin Kenyatta da ke birnin Nairobi, ya ce a asibitin kadai, jami’insu sun duba mutane 160 da suka samu raunukan harhasai wasu kuma kananan raunuka.

Ɗaya daga cikin abubuwan da masu zanga-zangar ke buƙata shi ne shugaban ƙasar William Ruto ya sauka daga muƙaminsa.

Matasan sun bayyana matakin gwamnatin Ruto na lafta wa jama’a haraji a matsayin wani sabon yunƙuri na jefa al’umma cikin ƙarin musiba, ganin yadda tuni matsalar tsadar rayuwa ta yi musu dabaibayi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like