Ƙasashen Waje
Paul Alexander, majinyacin da ke numfashi da huhun ƙarfe ya mutu
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/IMG_7306.jpeg)
Paul Alexander ya rasu ranar Litinin yana da shekaru 78, a cewar wata sanarwa da ɗan’uwansa, Philip Alexander, ya fitar ta kafar sada zumunta.
Paul Alexander, wanda ya mutu yana da shekaru 78 a duniya ya kamu da cutar shan inna yana da shekaru 6, ya kuma rayu na tsawon shekaru 70 yana numfashi ta wajen amfani da injin numfashi. Duk da haka, ya samu damar samun digiri na shari’a, ya kuma rubuta littafi.
Bayan da cutar shan inna ta shanye shi yana a shekara 6, lamarin ya tilastawa Paul Alexander dogara ga amfani da huhun ƙarfe.
Rayuwa a cikin huhun ƙarfe sakamakon kamuwa da cutar shan inna bai hana Alexander zuwa jami’a ba, ya samu digiri na shari’a da kuma aikin lauya fiye da shekaru 30 da suka shige. Lokacin da yake yaro, ya koya wa kansa numfashi na tsawon mintuna da sa’o’i a lokaci guda, duk da haka ya zama dole ya yi amfani da injin a kowace rana ta rayuwarsa.
Ya kasance ɗaya daga cikin mutane kaɗan da su ka rage a Amurka da ke zaune a cikin huhun ƙarfe. Kuma a cikin makonnin ƙarshe na rayuwarsa, ya nuna wa mabiyansa na TikTok yadda ya ke rayuwarsa da taimakon injin.
Ba a bayyana dalilin mutuwarsa a hukumance ba. Amma Alexander ya ɗan jima yana asibiti don ya kamu da cutar Covid-19 a watan Fabrairu, a cewar shafinsa na TikTok. Bayan ya koma gida, Alexander ya yi fama da rashin cin abinci da shan ruwa yayin da yake murmurewa daga cutar, wacce ke auka wa huhu kuma tana iya zama haɗari musamman ga mutanen da suka tsufa kuma suna da matsalar numfashi.
Alexander ya kamu da cutar shan inna a shekara ta 1952, a cewar littafinsa, “Three Minutes for a Dog: My Life in an Iron Lung.” wanda ya rubuta ta hanyar sanya Alƙalami ko fensir a bakinsa. Nan take likitocin asibitin Parkland da ke Dallas suka sanya shi cikin huhun ƙarfe domin ya samu yin numfashi.
Lokacin da yake cikin injin, Alexander yakan buƙaci taimakon wasu don ayyuka na yau da kullum kamar ci da sha.
KU KUMA KARANTA:Hukumar kwastom ta kama muggan ƙwayoyi da makamai a tashar jiragen ruwa na Legas
Alexander ya ƙaddamar da shafin TikTok ɗinsa a watan Janairu, kuma, tare da taimakon wasu, ya fara ƙirƙirar bidiyo game da rayuwarsa.
A cikin wani bidiyo, Alexander yayi cikakken bayani game da ƙalubalen tunani na rayuwa a cikin huhun ƙarfe.
“Akwai kaɗaici,” in ji shi “Wani lokaci ina cikin matsananciyar damuwa saboda ba zan ma iya taɓa wani ba, hannayena ba sa motsowa.”
Alexander ya faɗa a cikin bidiyon cewa ya shafe shekaru da dama yana samun saƙonnin imel da wasiƙu daga mutanen da ke fama da damuwa da kaɗaici, ya kuma ba su shawarwari.
Ƙasashen Waje
Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu
![Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240702-WA0041.jpg)
Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu
Daga Ibraheem El-Tafseer
Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.
A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.
A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.
KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki
Ƙasashen Waje
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza
![Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/5760.jpg)
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.
KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar
Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.
Ƙasashen Waje
Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC
![Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/20261902_0-387-5446-3067.jpeg)
Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC
Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.
Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.
COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.
COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.
Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.
KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya
Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.
Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano