Connect with us

Labarai

NURTW ta goyi bayan shugaba Tinubu kan cire tallafin man fetur

Published

on

Ƙungiyar ma’aikatan zirga-zirgar ababen hawa ta ƙasa (NURTW), ta yi alƙawarin bayar da cikakken goyon baya ga shirye-shirye da manufofin gwamnatin shugaba Bola Tinubu, a ƙoƙarinta na inganta rayuwar ‘yan Najeriya.

Shugaban ƙungiyar, Tajudeen Baruwa ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi ga shugabannin shiyyar na ƙungiyar da suka kai masa ziyarar haɗin kai, ranar Alhamis a Abuja.

Shugabannin shiyyar NURTW sun kaɗa ƙuri’ar amincewa da shugabancin Baruwa tare da yin alƙawarin goyon bayan takararsa na shugaban ƙungiyar a karo na biyu.

Shugaban NURTW ya samu wakilcin mataimakinsa na musamman kan hulɗar ƙwadago da masana’antu Abuul Boga.

KU KUMA KARANTA: Cire tallafin mai: Za mu sakawa ‘yan Najeriya da manyan ayyukan jin daɗin rayuwa – Tinubu

Baruwa ya ce ƙungiyar ta yi imanin cewa cire tallafin man fetur zai sa a samu ƙarin kuɗaɗe domin raya ƙasa, ciki har da sake gina titunan ƙasar nan da suka lalace.

Sai dai ya ce ƙungiyar za ta ci gaba da bayar da goyon bayan ƙungiyoyin ƙwadagon da ke buƙatar gwamnati don inganta tasirin cire tallafin man fetur ga ‘yan Najeriya.

Shugaban NURTW ya kuma jaddada buƙatar gwamnatocin jihohi musamman gwamnonin Kudu maso Yamma da su sake duba yadda za su maye gurbin NURTW da kwamitocin kula da wuraren shaƙatawa da garaje, PGMC.

Ya ci gaba da cewa ƙungiyar ta kasance ƙungiya ɗaya tilo da ta yi rijista ga direbobin kasuwanci a Najeriya.

“Saboda haka, muna so mu bayyana sarai, cewa kwamitin kula da wuraren shaƙatawa da garaji ba ƙungiyar ƙwadago ba ce da wata dokar ƙwadago ta sani a Najeriya.

“Ayyukan da suke yi ba bisa ƙa’ida ba ne kawai, har ma da ƙwace ayyukan ƙungiyar (NURTW).

“An shawarci ‘yan ƙungiyar da ke yankin Kudu maso Yamma da su rungumi ƙungiyar NURTW wadda ita ce ƙungiya ɗaya tilo da ta yi rajista kuma aka amince da ita ga duk direbobin ‘yan kasuwa a Najeriya.

“Hakazalika muna ƙira ga mutanen kudu maso yamma masu kishin ƙasa da su shiga tsakani, su kuma shawarci gwamnatocin jihohin da suka maye gurbin NURTW da PGMC, da su sake tunani.

“Muna ƙira gare su da su ƙyale ayyukan ƙungiyar a wuraren ajiye motoci da gareji daban-daban kamar yadda ake yi a wasu sassan ƙasar nan,” in ji shi.

Baruwa ya ƙara jaddada ƙudirinsa na kyautata rayuwar ‘ya’yan ƙungiyar, inda ya ƙara da cewa, shugabanni ya ƙaddamar da ƙarin kashi 100 na albashin ma’aikata da ƙarin girma ga ma’aikata da nufin ƙarfafa musu gwiwa.

Ya kuma ce ƙungiyar ta sake gyara babbar sakatariyar ƙasa da ta lalace zuwa matsayin ƙasa da ƙasa, wadda aka yi mata cikakkiya da na’urorin zamani. A cewarsa, hakan ya kasance don tabbatar da kyakkyawan yanayi ga jami’ai da ma’aikatan ƙungiyar.

“An samu ƙarin kashi 100 cikin 100 na alawus-alawus na ‘yan majalisar gudanarwa na ƙasa, shugabannin shiyyar, sakatarorin shiyya, sakatarorin jiha da ma’ajin jiha waɗanda su ma membobin majalisar zartarwa ne ta ƙasa ne.

“Za mu ci gaba da tabbatar da cewa ma’aikatanmu suna da ƙwarin gwiwa don samar da ayyukan yi da kuma ba su damar gudanar da aikin ƙungiyar,” in ji Baruwa.

Shugabannin shiyyar sun kaɗa ƙuri’ar amincewa da shugabancin ƙungiyar ta NURTW na ƙasa tare da yin alƙawarin goyon bayan zaɓen Baruwa a karo na biyu a matsayin shugaban ƙungiyar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: A bawa ɗalibai tallafin karatu, ba bashin kuɗin karatu ba – ƙiran ASUU ga gwamnatin tarayya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like