Connect with us

Labarai

NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Published

on

NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Daga Muhammad Kukuri 

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta ƙira taron gaggawa bayan Majalisar Zartaswa ta Tarayya ta jingine maganar karin mafi karancin albashi.

KƘungiyoyin ƙwadagon za su yi zaman ne da misalin karfe 10 na safiyar Laraba a Abuja, bayan matakin da Gwamnatin Tarayya ta jingine wasikar da ta fitar da farko kan karin mafi karancin albashin domin ba wa Shugaba Tinubu damar faɗaɗa tuntuɓar ɓangarorin da lamarin ya shafa.

Sun sanar da haka ne bayan Ministan Yada Labari da Wayar da Kan Al’umma, Mohammed Idris, ya sanar bayan taron Majalisar Zartaswa a ranar Talata cewa batun karin albashin ne kawai ba a tattauna a zaman da aka cimma matsaya kan abubuwa 39 da ke kunshe cikin ajandar taron ba.

Ministan ya bayyana cewa kafin zaman an karɓi rahoton kwamitin karin albashin da ya kunshi matakan gwamnati uku da kungiyar kwadago da kuma kamfanoni masu zaman kansu.

KU KUMA KARANTA: Majalisar Zartaswa ta jingine batun ƙarin mafi ƙarancin albashi

Sai dai, a cewarsa, Majalisar Zartaswa ta jingine aiwatar da umarnin karin mafi karancin albashin ne saboda al’amarin ya shafi duk bangarorin — gwamnatocin tarayya, jihohi da kananan hukumomi, kamfanoni masu zaman kansu da ’yan kwadago.

A cewarsa a yi hakan ne domin Shugaba Bola Tinubu ya kara tuntubar masu ruwa da tsaki kafin mika lamarin ga Majalisar Dokoki ta Kasa.

Bayan nan ne wani jigon a ƙungiyar NLC ya tabbatar wa Aminiya a daren Talata cewa shuagabancin kungiyoyin zai yi zaman gaggawa domin cimma matsaya kafin shugaban kasa ya tuntube su yi kan lamarin.

“Duk da cewa mun riga mun yanke shawara, amma za mu sake zama ranar Laraba da safe domin sake duba lamarin kafin su (gwamnati) tuntube mu.

“Zaman na da muhimmanci,” inji babban jami’in na ƙungiyar ƙwadago.

A farkon watan nan na Yuni ne ƙungiyoyin kwadago suka shiga yajin aikin kwana biyu da ya tsayar da harkoki cak a Najeriya.

Sun yi yajin aikin ne domin neman ƙarin mafi ƙarancin albashin da har yanzu ake ci gaba da kai ruwa rana tsakaninsu da ɓangaren gwamnati.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like