Connect with us

Labarai

NLC ta ayyana yajin aikin gargaɗi na kwana biyu kan cire tallafin mai

Published

on

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta fara shirin yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyu daga ranar Talata 5 ga watan Satumba, domin nuna adawa da gwamnatin tarayya kan gazawarta na magance ƙalubalen da ke haifar da cire tallafin man fetur.

Shugaban ƙungiyar ta NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin da yake ganawa da manema labarai a gidan ma’aikata da ke Abuja, yayin da yake magana kan ƙudurin da kwamitin gudanarwa na NLC ya yi a ranar da ta gabata.

Ƙungiyar ƙwadagon dai na zargin gwamnatin tarayya da yin watsi da tattaunawar da kuma ka sa aiwatar da wasu ƙudurorin da suka cimma da gwamnatin a baya.

A ranar 2 ga watan Agusta, ƙungiyoyin ƙwadago sun nuna rashin amincewarsu da abin da suka bayyana a matsayin manufofin gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

KU KUMA KARANTA: Hukumar ‘yan Sanda sun gargaɗi NLC kan zanga-zangar da suka shirya yi

Ƙungiyoyin ƙwadagon Najeriya (NLC), Trade Union Congress (TUC) da ƙungiyoyinsu sun gudanar da zanga-zanga a babban birnin tarayya Abuja da jihohi da dama da suka haɗa da Legas, Abiya, Filato, Kaduna, Kano, Ribas, Zamfara, Katsina, Kuros Riba, Ebonyi, Inugu, Kwara, Ogun, Imo, Ondo, da Edo.

Zanga-zangar ta biyo bayan wa’adin kwanaki bakwai da aka bawa gwamnatin tarayya na neman “a gaggauta sauya duk wasu manufofin gwamnatin tarayya na yaƙi da talauci da suka haɗa da ƙarin farashin PMS (Premium Motor Spirit) da aka yi a baya-bayan nan, da ƙarin kuɗin makarantar gwamnati, da sakin watanni takwas da aka hana albashin malaman jami’a da ma’aikata”.

Ƙungiyar ta kuma buƙaci a sake duba mafi ƙarancin albashi daga N30,000 zuwa N200,000, tana mai cewa tun lokacin da Shugaban ƙasa ya yi jawabin rantsar da “Shugaban ƙasa” a ranar 29 ga Mayu, 2023, hankalin ‘yan Najeriya ya tashi.

Taro da dama da fadar shugaban ƙasa da ƙungiyoyin ƙwadago suka yi kan tallafin da ‘yan Najeriya ke fama da su sakamakon cire tallafin man fetur ya ci tura.

A watan da ya gabata, shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayar da hujjar cewa Naira biliyan 5 da aka amince wa kowace jiha da kuma babban birnin tarayya Abuja don rage tasirin cire tallafin man fetur bai isa ya yi tasiri ga jama’a ba.

Da yake bayyana a gidan talabijin na Channels Television’s Politics Today wanda ‘News Point Nigeria’ a ranar 18 ga watan Agusta ke sa ido a kai, Ajaero ya ce idan aka ƙididdige Naira biliyan 5 ba za ta kai Naira 1,500 ga kowane mutum ba.

A cewar sa, babu tabbas kan ko kuɗin rance ne ko kuma na jin daɗi ga jihohi ko kuma ga ‘yan Najeriya.

“Haɗin farko na farashin man fetur da kuma na ƙarshe ya motsa mutane da yawa daga kan iyaka zuwa matsanancin talauci,” in ji shi.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Likitoci a Zamfara sun dakatar da shiga yajin aiki | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Katsewar wutar lantarki sakamakon yajin aikin gargaɗin NLC – AEDC | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like