Connect with us

Labarai

NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Published

on

NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Daga Muhammad Kukuri 

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta ƙira taron gaggawa bayan Majalisar Zartaswa ta Tarayya ta jingine maganar karin mafi karancin albashi.

KƘungiyoyin ƙwadagon za su yi zaman ne da misalin karfe 10 na safiyar Laraba a Abuja, bayan matakin da Gwamnatin Tarayya ta jingine wasikar da ta fitar da farko kan karin mafi karancin albashin domin ba wa Shugaba Tinubu damar faɗaɗa tuntuɓar ɓangarorin da lamarin ya shafa.

Sun sanar da haka ne bayan Ministan Yada Labari da Wayar da Kan Al’umma, Mohammed Idris, ya sanar bayan taron Majalisar Zartaswa a ranar Talata cewa batun karin albashin ne kawai ba a tattauna a zaman da aka cimma matsaya kan abubuwa 39 da ke kunshe cikin ajandar taron ba.

Ministan ya bayyana cewa kafin zaman an karɓi rahoton kwamitin karin albashin da ya kunshi matakan gwamnati uku da kungiyar kwadago da kuma kamfanoni masu zaman kansu.

KU KUMA KARANTA: Majalisar Zartaswa ta jingine batun ƙarin mafi ƙarancin albashi

Sai dai, a cewarsa, Majalisar Zartaswa ta jingine aiwatar da umarnin karin mafi karancin albashin ne saboda al’amarin ya shafi duk bangarorin — gwamnatocin tarayya, jihohi da kananan hukumomi, kamfanoni masu zaman kansu da ’yan kwadago.

A cewarsa a yi hakan ne domin Shugaba Bola Tinubu ya kara tuntubar masu ruwa da tsaki kafin mika lamarin ga Majalisar Dokoki ta Kasa.

Bayan nan ne wani jigon a ƙungiyar NLC ya tabbatar wa Aminiya a daren Talata cewa shuagabancin kungiyoyin zai yi zaman gaggawa domin cimma matsaya kafin shugaban kasa ya tuntube su yi kan lamarin.

“Duk da cewa mun riga mun yanke shawara, amma za mu sake zama ranar Laraba da safe domin sake duba lamarin kafin su (gwamnati) tuntube mu.

“Zaman na da muhimmanci,” inji babban jami’in na ƙungiyar ƙwadago.

A farkon watan nan na Yuni ne ƙungiyoyin kwadago suka shiga yajin aikin kwana biyu da ya tsayar da harkoki cak a Najeriya.

Sun yi yajin aikin ne domin neman ƙarin mafi ƙarancin albashin da har yanzu ake ci gaba da kai ruwa rana tsakaninsu da ɓangaren gwamnati.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like