No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Jamhuriyar Nijar ta sake buɗe kan iyakarta da Najeriya a yankunan Diffa da Tahoua da Maraɗi da Dosso.

An rufe iyakar ƙasar da ke tsakanin maƙwabtan biyu biyo bayan juyin mulkin da aka yi a ranar 26 ga watan Yuli da kuma takunkumin da ƙungiyar ECOWAS ta ƙaƙaba mata.

A wani saƙon rediyo da aka watsa a shafukan sada zumunta, a ranar Alhamis, ma’aikatar harkokin cikin gida ta Jamhuriyar Nijar ta umurci gwamnonin waɗannan yankuna na kan iyaka da su ba da izinin sake buɗe aiki da ƙarfe 12:00 na dare.

Ma’aikatar ta kuma umurci gwamnonin da abin ya shafa da su ƙarfafa tsaro a kan iyakokin ƙasar.

KU KUMA KARANTA:Shugaba Tinubu ya ba da umarnin buɗe iyakokin Najeriya da Nijar nan-take

An buɗe iyakokin Najeriya makonnin da suka gabata bayan ɗage takunkumin da ƙungiyar ECOWAS ta ƙaƙaba wa ƙasar a wani taro da aka yi a Abuja, amma Nijar ba ta mayar da martani ba nan take.

Sai dai kuma har yanzu kan iyakar Nijar da maƙwabciyar Benin na nan a rufe a ɓangaren Nijar duk da gaggawar aiwatar da umarnin ECOWAS da hukumomin Benin suka yi.

Hukumomin riƙon ƙwaryar Nijar sun bayar da dalilai na tsaro a matsayin dalilin rashin buɗe kan iyaka da maƙwabtanta da ke Kudu.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...