No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Reshen Siyasa na ƙungiyar Hamas, Ismail Haniyeh ya yi gargaɗi kan yiwuwar mamayar soji daga sojojin Isra’ila a Rafah, kuma ya ce haka zai iya haifar da kisan kiyashi kan Falasɗinawa.

A wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Anadolu ranar Asabar, Haniyeh ya ce, “Ina kira da duka ƙasashe ƙawayenmu, da ‘yan’uwanmu a Masar, da ‘yan’uwanmu a Turkiyya, da ‘yan’uwanmu a Qatar a matsayin masu shiga-tsakani, da ƙasashen Turai da su ɗauki matakin hana zaluncin (Isra’ila), don dakatar da hari kan Rafah, da kuma ficewar (sojin Isra’ila) gaba ɗaya daga Zirin Gaza da kawo ƙarshen hare-hare kan Gaza”.

KU KUMA KARANTA: Hamas da Islamic Jihad sun bayar da sharuɗa 4 na nasarar yarjejeniyar tsagaita wuta

Game da fafutukar Falasɗinawa, Haniyeh ya ce, “Idan maƙiyanmu ‘yan aƙidar Zionism suka shiga Rafah, al’ummar Falasɗinu ba za su zaɓi ajiye makami ba. Mayaƙanmu a Rafah sun shirya kare kansu da tirjiya ga azzalumai.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...