No menu items!

Sample Page Title

Date:

NDLEA ta kama wani babban dilan ƙwaya a Kano

Daga Jameel Lawan Yakasai

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), reshen jihar Kano, ta ce ta kama wani fitinannen dilan miyagun kwayoyi, Faisal Yusuf Umar, mai shekaru 23, a Ƙaramar Hukumar Fagge.

KU KUMA KARANTA: NDLEA ta kama maniyyata a filin jirgin saman Kano, bisa zargin safarar hodar Iblis zuwa ƙasar Saudiyya

Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sadiq Muhammad Maigatari ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano a yau Lahadi.

Ya ce an kama wanda ake zargin ne bayan wani binciken sirri da aka gudanar sakamakon koken al’umma game da miyagun ayyukansa.

“A ranar 18 ga watan Yuli, jami’an NDLEA da ke ƙarƙashin rundunar, reshen Fagge sun gudanar da wani sintiri na musamman a gidan su wanda ake zargin da ke Dandali, a Ƙaramar Hukumar Fagge.

“An samu tarin kayan maye, ciki har da kwalabe 40 (kilo 4) na maganin tari na Benylin mai ɗauke da Codeine, tare da kuɗi har naira 204,000.00,” in ji shi.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...