Connect with us

Labarai

NDLEA ta kama ƙwayoyin Tramol da Exol-5 a jihohi uku na arewa

Published

on

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA), ta kama wasu ƙwayoyin Tramadol da suka kai 122,900 da Exol-5 a jihohin Bauchi, Kano da Benue.

Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja, inda ya ce an gano ƙwayoyin Tramadol dubu 87,000 daga hannun wani da ake zargi, Tony Ogbonna, mai shekaru 40, a unguwar Yelwa da ke Bauchi, a ranar 17 ga watan Yuni.

Mista Babafemi ya ƙara da cewa, ƙwayoyin tramadol dubu 13,800 da wani da ake zargi ya yi watsi da su zuwa Geidam a Yobe, an kuma gano su a filin shaƙatawa na ‘Yankaba a Kano, a ranar 14 ga watan Yuni.

KU KUMA KARANTA: NDLEA ta bankaɗo ɗakin da ake haɗa sinadaran ƙwayar meth, ta ƙwato fakitin haramtattun ƙwayoyi da dama

Mista Babafemi ya ce a wannan rana a Benue, an kama wani da ake zargi, Chidera Gabriel da ƙwayoyi guda dubu 22,100 na maganin ‘opioid’ a wani wurin duba lafiyar NDLEA a Vandeikya.

Kakakin hukumar ta NDLEA ya bayyana cewa jami’an hukumar a Kaduna sun kama wata mata mai suna Pharmacist Ikwebe Ori.

Mista Babafemi ya ce kamen ya biyo bayan yunƙurin da ta yi na yin amfani da takardun jabu wajen siya tare da rarraba kwali shida na allurar pentazocine tare da kwalabe guda dubu 2,000.

“Ta yi iƙirari cewa ta yi amfani da takardun ƙarya na wani asibitin Kaduna wajen ba da odar maganin, wanda ta shirya rarrabawa a Kaduna, Abuja da Sokoto.

“Da farko an kama kayan ne a reshen filin jirgin sama na Murtala Muhammed International Airport (MMIA), Ikeja yayin da wani jami’in sufuri ya tura shi Kaduna,” inji shi.

Hakazalika, jami’an hukumar NDLEA a Jamhuriyar Nijar sun kama jimillar tabar wiwi kilogiram dubu 1,072 a samame guda biyu. Babafemi ya ce an gano kilogram ɗari 726 na haramtattun kayan a gidan man Oyoyo da ke kan titin Kaduna zuwa Abuja a ranar Alhamis, 15 ga watan Yuni.

“Mutane huɗu da ake zargi: Aminu Mohammed, 50; Nasiru Mohammed, 30; Rabiu Haruna mai shekaru 29 da Hamza Abubakar mai shekaru 18 an kama su.”

A cewarsa, a ranar 16 ga watan Yuni, jami’an tsaro sun kama wata mota ƙirar Mercedes 1422 mai lamba MKD 116 ZM a kan hanyarta daga Umunede jihar Delta ɗauke da galan na dabino da za a kai a kasuwar Garki da ke Abuja.

“Duk da haka, direban babbar motar mai suna Jekwe Udenze, mai shekaru 38, tare da mataimakansa guda biyu: Gabriel Nzekwube, mai shekaru 43, da Chima Uzoma, mai shekaru 42, sun tsaya a Uromi, Edo.

“Sun kwashe buhunan tabar wiwi guda 19 mai nauyin kilogiram 346, inda za a kai su a Dumez Luxury Park da ke kan titin Kaduna, Suleja ga wani Ignatius Mokwe mai shekaru 47.

“An kama direban da mataimakansa biyu da kuma mai haramtaccen kayan, Ignatius Mokwe,” in ji shi.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Hukumar NDLEA ta kama mutane 420 da ake zargi da sayar da miyagun ƙwayoyi a Kaduna | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like