No menu items!

Sample Page Title

Date:

NBC ce ke da hurumin dakatar da Bategi FM ba Gwamnatin Neja ba – Minista

Daga Jameel Lawan Yakasai

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan al’umma na Najeriya, Muhammad Idris Malagi ya buƙaci kowane ɓangare ya mayar da kubensa kan batun rufe gidan rediyon Badegi FM da ke birnin Minna a jihar Neja.

Ministan ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Rabiu Ibrahim ya fitar, inda a ciki ya ce hukumar kafafen watsa labarai ta Najeriya wato NBC na da hanyoyin shiga tsakani idan aka samu irin wannan matsalar.

Rahotanni sun nuna cewa Gwamnan jihar Neja, Umaru Bago ya bayar da umarnin rufe gidan rediyon ne a lokacin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC na jihar a ranar 1 ga watan Agusta.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin tarayya ta jaddada ƙudirin kare ‘yancin ‘yan jarida da ‘yancin faɗin albarkacin baki

Gwamnan ya zargi gidan rediyon ya karya dokokin watsa labarai, da kuma tunzura mutane a kan gwamnatin jihar.

“Duk da cewa mun fahimci abin da gwamnatin ke zargi, ma’aikatar watsa labarai na so a fahimci cewa Hukumar NBC ce ke da hurumin dakatar da lasisin gidan rediyo Gwamnatin Neja ba, kamar doka ta tanada.

“Don haka ne ma’aikatar ke kira ga gwamnatin jihar Neja da ta kai ƙorafinta ga NBC kan gidan rediyon NBC bisa zargin “karya doka” da take yi wa gidan rediyon.”

A ƙarshe ministan ya yi kira da a bi lamarin a hankali, inda ya tabbatar da cewa NBC za ta yi aikin da ya dace domin tabbatar da sasanci kan lamarin.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...