No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ma’aikatan aikewa da saƙonni ta Nijeriya (NIPOST), sun rufe babban ofishin hukumar da ke Abuja, suna zanga-zangar nuna adawa da naɗin Tola Odeyemi a matsayin babban jami’in gudanarwa a hukumar.

Ajuri Ngelale, mai magana da yawun shugaban ƙasa, ya bayyana a makon da ya gabata cewa, shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya yi wasu sauye-sauye a shugabancin hukumomin sadarwa da suka haɗa da NIPOST.

Sai dai jim kaɗan bayan da labarin naɗin Odeyemi ya ɓulla, an samu rahotannin cewa an mayar da Adeyemi Adepoju, wanda aka kora daga muƙamin babban jami’in gudanarwar hukumar.

A cikin wani faifan bidiyo, an ga Adepoju yana jawabi ga wasu ma’aikata da suka yi iƙirarin cewa Tinubu ya sake naɗa shi.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya naɗa jigon ɗan PDP a matsayin shugaban FERMA

Sai dai a ranar Litinin ma’aikatan sun yi zanga-zangar sun kuma hana sabuwar shugabar hukumar ta NIPOST shiga ofishin hukumar, inda suka ce naɗin nata ya saɓa wa muradinsu.

Ma’aikatan, waɗanda suka ce sun fi son Adepoju, sun rera waƙoƙin haɗin kai, ɗauke da allunan nuna rashin amincewa da sabon naɗin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...