Connect with us

Labarai

Nan da mako huɗu Najeriya za ta daina sayo man fetur daga waje — Ɗangote

Published

on

Nan da mako huɗu Najeriya za ta daina sayo man fetur daga waje — Ɗangote

Nan da shekara uku zuwa huɗu nahiyar Afirka ba za ta sake sayen takin zamani daga waje ba.

Matatar man Dangote da ke Jihar Legas ta ce Najeriya za ta daina sayo man fetur daga waje a watan Yuni, a ƙoƙarin da ƙasar ke yi na samun dogaro da kai a fannin makamashi.

Mai matatar, Alhaji Aliko Ɗangote shi ne ya bayyana haka a taron kolin shugabannin kamfanoni na Afirka ranar Juma’a a Kigali, babban birnin Rwanda.

Hamshakin attajirin ya ce, matatar za ta samar da man da ake bukata a cikin gida ba ga Najeriya ba kadai har ma da sauran kasashen yankin Afirka ta yamma.

KU KUMA KARANTA: Ɗalibi ya lashe N5 miliyan a tallan siminti na Dangote

Ɗangote ya ce, a cikin watan Yuni, wato nan da mako huɗu zuwa biyar, ba wani mai da Najeriya za ta rika saye daga waje.

“A yanzu Najeriya ba ta buƙatar shigo da wani man fetur kuma zuwa wani lokaci a watan Yuni, nan da makonni huɗu ko biyar masu zuwa, bai kamata Najeriya ta ƙara shigo da wani abu mai suna man fetur ba, ko da kuwa ɗigon lita ɗaya ne.

“Muna da isasshen man fetur da dizel da za mu ba aƙalla Afirka ta Yamma da Afirka ta Tsakiya.

“Muna da isasshen man jirgin da za mu ba duk nahiyar Afirka da kuma fitar da shi zuwa Brazil da Mexico.

Ya kara da cewa: “Matatar mu tana da girma sosai, kuma wannan abu ne da muka yi imani cewa Afirka na buƙata.

“Abin takaici idan aka dubi nahiyar Afirka baki ɗaya, ƙasashe biyu ne kawai ba sa shigo da man fetur — daga Aljeriya sai Libya kawai — amma ragowar duk suna shigo da shi ne.

“Don haka, ya kamata mu sauya wannan tsari mu tabbatar da cewa ba wai kawai mu je muna haƙo ɗanyen man fetur ba, ya kamata mu riƙa tace wanda zai wadatar da mu a nan cikin gida kuma a samar da ayyukan yi.”

Bayan man fetur, Dangote ya ce matatar za ta kuma samar da isasshen man dizil ga Afirka ta yamma da ma Afirka ta tsakiya.

Haka kuma ya ce, matatar za ta iya samar da isasshen man jirgin sama ga nahiyar Afirka gaba daya, har ma ta fitar da shi zuwa kasashen Brazil da Mexico.

Attajirin wanda ya fi kowa kudi a Afirka ya kuma bayyana cewa, nan da shekara uku zuwa huɗu nahiyar Afirka ba za ta sake sayen takin zamani daga waje ba, domin matatar za ta wadata nahiyar da takin.

Matatar man ta Dangote bayan soma aiki a watannin bayan nan na iya tace gangar ɗanyen mai 650,000 duk rana, kuma idan ta fara aiki ɗari bisa ɗari za ta zama mafi girma a Afirka da Turai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like