No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Kakakin majalisar wakilan Najeriya, Tajudeen Abbas ya ce majalisar na sane da halin matsalar tsaro da tsadar rayuwa da ‘yan ƙasar ke fuskanta.

Honarabul Tajudeen Abbas ya ce a ɓangarensu na majalisa ba za su zuba wa ɓangaren zartaswa ido ba har sai an samu mafita.

Kakakin majalisar ya tabbatar wa da BBC cewa za a shawo kan ƙalubalen da ake fuskanta nan ba daɗewa ba.

”Majalisa za ta yi duk abin da ya kamata domin ganin an samu sauƙi a matsalar tsaro da tsadar rayuwa da ke fuskanta a ƙasar nan”.

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta nemi taimakon Faransa kan matsalar tsaro

Kakakin majalisar ya ce majalisa ta za ƙirawo duka masu ruwa da tsaki a harkar tsaro domin magance matsalar tsaron da ake ciki.

Honarabul Tajedeen Abbas ya ce ‘yan majalisar na sane da irin halin matsin rayuwa da talakawan ƙasar ke ciki, kuma suna duk mai yiwuwa domin magance matsalar.

Don haka ne ma ya ce ‘yan majalisar suka mayar da hankali wajen sayen kayan abinci domin rabar wa talakwan da suka zaɓe su.

Ya kuma ce gwamnati na yin duk mai yiwuwa don magance matsalar, kuma ya tababtar da cewa nan ba da jimawa ba farashin kayan abincin zai sauka a ƙasar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...