No menu items!

Sample Page Title

Date:

NAFDAC ta buƙaci a zartar da hukuncin kisa kan masu fataucin ƙwaya

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta Najeriya (NAFDAC) ta ba da shawarar zartar da hukuncin kisa akan masu fataucin ƙwaya.

A cewar babbar daraktar hukumar, Mojisola Adeyeye, tsattsauran hukunci ne kawai zai dakatar da fataken kwaya musamman ma yadda take sanadiyar mutuwar kananan yara.

KU KUMA KARANTA:NAFDAC ta lalata kayayyakin jabu na Naira biliyan 1.3 a Abuja

Shugabar hukumar ta NAFDAC ta kuma nemi hadin kan bangaren shari’a da majalisar kasa wajen ganin wannan buri ya zama gaskiya.
A cewarta, a shirye hukumar take ta yi hadin gwiwa da ‘yan majalisa da sauran masu ruwa da tsaki a kan batun, inda Adeyeye ta koka da karancin ma’aikata a hukumar.

Ta yi amannar cewar da ma’aikata kimanin 2, 000 a fadin Najeriya da karancin kudade, babu yadda za’a yi NAFDAC ta gudanar da ayyukanta yadda ya dace.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...