No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce shi da kansa ya zaɓi ya bayyana cire tallafin man fetur a ranar farko da ya zama shugaban ƙasa duk da cewa ba a rubuta shi ba a cikin jawabin da ya gabatar.

Shugaban ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da ‘yan Najeriya mazauna Faransa ranar Juma’a, kamar yadda mai ba shi shawara kan ayyuka na musamman Dele Alake ya faɗa cikin wata sanarwa.

Sanarwar ta ce: “Tinubu ya yi bayani cewa mai ba shi shawara kan harkokin kuɗi Wale Edun, da mai ba shi shawara kan ayyuka na musamman Dele Alake ba su saka maganar cire tallafi ba a jawabinsa, amma ya ji cewa ya kamata ya kawo ƙarshensa a ranar farko.”

Shugaban ya kuma bayyana tallafin a matsayin “zamba” da ke “hana cigaba” yayin ganawar tasa da ‘yan Najeriya.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya ba da umarnin mayar da NEMA, NAHCON ƙarƙashin ofishin mataimakin shugaban ƙasa

Tun daga ranar 29 ga watan Mayu da Tinubu ya sanar da cewa “tallafin man fetur ya tafi” farashin man ya ninninka, inda ake sayar da lita ɗaya kan Naira ɗari 540 zuwa sama saɓanin N195 da aka saba sayarwa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...