Mutum 40 a Kebbi sun ɓace bayan kifewar kwale-kwale

Kimanin mutum 40 ne ake zullumin sun ɓace bayan wani hatsarin kwale-kwale a yankin ƙaramar hukumar Yauri a Jihar Kebbi.

Aminiya ta gano cewa kwale-kwalen ya yi hatsari ne yayin da yake ɗauke da kaya da fasinjoji kimanin 50 a kan Kogin Neja a rnaar Litinin.

Shugaban ƙaramar hukuumar Yauri, Alhaji Bala Mohammed, ya ce fasinjojin da kwale-kwalen sun taso ne daga ƙauyen Kasabo a ƙaramar Hukumar Agura na Jihar Neja a hanyarsu ta zuwa Yauri inda suka yi hatsari.

Ya ce hatsarin kwale-kwale ya auku ne sakamakon ƙarfin igiyar ruwa, kuma mutum 10 ne aka yi nasarar ceto wa zuwa lokacin da muka samu wannan rahoto.

Amma ya ce “ana ci gaba da aikin ceto” da fatan sauran ma za a same su da ransu.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *