No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mutum 4 sun jikkata a Filato sakamakon rushewar wani gini

Mutane huɗu sun jikkata sakamakon rushewar gini a yankin Ƙaramar Hukumar Riyom da ke Jihar Filato.

Rushewar ginin ya auku ne a kusa da Kwalejin Gwamnati da ke garin Riyom safiyar Litinin, kamar yadda rahotanni suka nuna.

Wani mazaunin garin, Dusu Joseph, ya ce “ba a samu asarar rai ba, amma yawancin waɗanda suka samu rauni ƙananan yara ne kuma an kai su asibiti domin duba lafiyarsu.”

KU KUMA KARANTA: Mutum 3 sun mutu a Legas bayan rushewar gini

Shi kuma wani mai suna Bot Rwang, godiya ga Allah ya yi bisa yadda iyalan da ke cikin gidan da ya ruguje suka tsallake rijiya da baya, babu asarar rai.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...