Connect with us

Ƙasashen Waje

Mutum 15  sun mutu a harin da ƴan bindiga suka kai coci a Burkina Faso

Published

on

Fararen-hula aƙalla 15 ne suka mutu sannan biyu suka jikkata a wani harin “ta’addanci” da aka kai a cocin Katolika da ke arewacin Burkina Faso ranar Lahadi, a cewar wani babban jami’in cocin.

“Muna sanar da ku cewa an kawo harin ta’addanci a cocin Katolika da ke ƙauyen Essakane yau, 25 ga watan Fabrairu, yayin da mutane suka haɗu suna gudanar da ibada,” in ji shugaban cocin Dori, Jean-Pierre Sawadogo, a wata sanarwa da ya aike wa kamfanin dillancin labarai na AFP.

Ya ƙara da cewa mutanen da suka mutu sun kai 15 sannan mutum biyu sun jikkata.

Sawadogo ya yi ƙira da a zauna lafiya a Burkina Faso sannan ya soki waɗanda ya ƙira “mutanen da ke ci gaba da kashe jama’a da raba kan ƙasarmu”.

KU KUMA KARANTA: Mali da Burkina Faso sun miƙa wa ECOWAS wasikar ficewarsu

Ƙauyen Essakane yana kan iyakar ƙasar da Mali da Jamhuriyar Nijar.

Wannan shi ne hari na baya bayan nan da ake ɗora alhakin kai shi kan ƙungiyoyin da ke iƙirarin jihadi a yankin, waɗanda kan kai hare-hare a coci-coci sannan a wasu lokutan suna sace malaman cocin.

Burkina Faso na da faɗin ƙasa a yankin Sahel, inda masu iƙiradin jihadi suka matsa ƙaimi wajen kai hare-hare tun bayan faɗuwar gwamnatin Libya a 2011 da kuma ƙwace iko da masu iƙirarin jihadi suka yi da arewacin Mali a 2012.

Waɗannan hare-hare sun watsu zuwa maƙwabciyarsu Jamhuriyar Nijar.

Shugaban mulkin sojin ƙasar Kyaftin Ibrahim Traore, wanda ya ƙwace mulki a 2022, ya sha alwashin murƙushe masu tayar da ƙayar baya, amma har yanzu lamarin ya gagara.

Alƙaluma sun nuna cewa an kashe mutum fiye da 20,000 a hare-haren da masu tayar da ƙayar baya suke kai wa Burkina Faso sannan an raba sama da mutum miliyan biyu da muhallansu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like