No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mutanen da Isra’ila ta kashe a Gaza sun ƙaru – Rahoto

Adadin mutanen da suka rasa rayukansu a hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai a Gaza tun daga ranar 7 ga watan Oktoban 2023, ya ƙaru da 28 a cikin sa’o’i 24 da suka wuce, inda yawan ya kai 44,786.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Lafiya ta Falasɗinu a Gaza ta fitar, an bayar da bayanai dangane da hare-haren da Isra’ila ke kai wa Gaza tsawon kwanaki 431.

An bayar da rahoton cewa, mutume 28 ne suka rasa rayukansu kana wasu 54 kuma suka samu raunuka sakamakon kisan kiyashi huɗu da sojojin Isra’ila suka yi a sassa daban-daban na Gaza cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

KU KUMA KARANTA: Masu zanga-zanga a Isra’ila sun zargi Netanyahu da ƙin kawo ƙarshen yaƙin da ƙasar ke yi a Gaza

An yi kiyasin cewa adadin mutanen da suka rasa rayukansu a hare-haren da Isra’ila ke kaiwa Gaza tun daga ranar 7 ga watan Oktoban 2023, ya ƙaru zuwa 44,786 sannan adadin waɗanda suka jikkata ya ƙaru zuwa 106,188

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...