Connect with us

Ƙasashen Waje

Mutane sama da dubu biyu ne suka mutu a Libya, sakamakon ambaliyar ruwan sama

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Yawan mutanen da suka mutu sanadin ambaliyar ruwa a ƙasar Libya ya ƙaru zuwa sama da 1,500 a birni guda ɗaya kawai, a cewar ministan da ya kai ziyara Derna, birnin gaɓar teku.

“Na kaɗu game da abin da na gani, tamkar ambaliyar tsunami,” Hisham Chkiouat, daga gwamnatin da ke sansani a gabashin ƙasar, ya ce.

Ruwa ya shafe mafi yawan sassan birnin Derna, wanda matsuguni ne ga mutane kimanin 100,000, bayan madatsun ruwa guda biyu da gadoji huɗu suka karye.

Sama da mutum 10,000 ne aka ba da rahoton cewa sun ɓata bayan gawurtacciyar guguwar da aka yi laƙabi Daniel ta auka, kamar yadda ƙungiyar ba da agaji ta Red Cross ta ba da rahoto.

KU KUMA KARANTA: Akwai barazanar ambaliyar ruwa a jihohi takwas a Najeriya – NEMA

Guguwar wadda ta auka wa ƙasar ranar Lahadi, ta kuma shafi biranen gabashin Libya, kamar Benghazi da Soussa da Al-Marj.

Hashem Chkiouat, ministan sufurin jiragen sama kuma ɗan kwamitin kai ɗauki na gwamnatin gabashin ƙasar ya faɗa wa BBC cewa karyewar ɗaya daga cikin madatsun ruwan da ke kudancin Derna, ya sa ruwa ya janye sassan birnin zuwa cikin teku.

Adadin mutanen da suka mutu gaba ɗaya, mai yiwuwa ne zai ƙaru fiye da haka.

“Ban zuzuta maganata ba, idan na cewa kashi ɗaya cikin huɗu na birnin ya ɓace. Gidaje da yawa, masu yawa nake faɗa muku, sun ruguje.”

Biranen gabashi irinsu, Benghazi da Sousse da kuma Al-Marj, su ma duk abin ya shafe su.

Tun da farko, Firaministan Osama Hamad ya faɗa wa wata tashar talbijin ɗin Libya cewa sun ƙiyasta mutane kimanin 2,000 ne suka mutu yayin da wasu dubbai kuma suka ɓace: “Unguwanni gaba ɗaya a birnin Derna sun ɓace, tare da mazaunansu… duka ruwa ya awon gaba da su.”

Tare da sauran yankunan gabashin ƙasar, birnin Misrata da ke yammacin Libya na cikin sassan da ambaliyar ruwan ta aukawa.

Ruwan sama ya haddasa mummunar ambaliya tare da zaftarewar ƙasa da kuma lalata gidaje da tituna da dama.

An ayyana yankin Derna a matsayin wanda mummunan bala’i ya aukawa, sannan an yi shelar zaman makoki na kwana uku.

Bayanai sun nuna cewa abu ne mai wuya a iya bayyana yawan mutanen da suka halaka, saboda babu hanyoyin sadarwa sosai.

Sannan kuma ga rashin tartibiyar gwamnati, sakamakon yaƙin da aka kwashe wajen shekara goma ana yi, tsakanin manyan abokan gaba biyu a ƙasar.

Sojojin ƙasar ta Libya bakwai ne aka bayar da rahoton sun ɓace a lokacin da suke gudanar da aikin agaji.

Jami’ai a gabashin ƙasar da ke ƙarƙashin ikon gwamnatin da ƙasashen duniya ba su amince da ita ba sun ayyana dokar hana fita, yayin da suka bayar da umarnin rufe makarantu da shaguna.

An sa dokar hana fita da kuma makoki na kwana uku a gabashin ƙasar

Masana sun yi gargaɗin cewa sauyin yanayi na duniya na nufin za a samu ƙaruwar tururi a lokacin bazara, wanda hakan zai haddasa mamakon ruwan sama da iska.

A yanzu mahaukaciyar guguwar mai tafe da mamakon ruwan saman ta isa yammacin Masar.

Ma’aikatar harkokin wajen Turkiyya ta ce za ta tura jiragen sama uku da za su kai ma’aikatan agaji da kuma kayan taimako zuwa ƙasar ta Libya.

Tun shekara ta 2014 Libya ke ƙarƙashin mulkin abokan gabar biyu bayan kashe daɗaɗɗen shugaban ƙasar Muammar Gaddafi a 2011.

Gwamnatin Firaminista Fayez al-Serra wadda ke samun goyon bayan majalisar ɗinkin duniya na yaƙi da tawayen Janar Khalifa Haftar wanda ƙasashe da hukumomin duniya ba su amince da mulkinsa ba kuma yake riƙe da iko a yankin gabashin ƙasar.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Abubuwan da ya kamata a sani game da sabuwar wayar iPhone 15 - LEGEND FM DAURA

  2. Pingback: Ana ci gaba da jimamin waɗanda suka mutu a ambaliyar ruwa a Libya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like