No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mutane huɗu ne suka rasa rayukansu sakamakon wani hatsarin mota da ya auku a babbar hanyar Ibadan zuwa Oyo a ranar Asabar.

Wasu da dama kuma sun jikkata a cikin motar bas da hatsarin ya rutsa da su yayin da ta yi taho mu gama da su.

Kwamandan rundunar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) a Atiba, Oyo, DCC Bayode Olugbesan, ya ɗora alhakin hatsarin da gudun wuce gona da iri.

Mista Olugbesan ya ce motar bas mai mutane 14 tana ɗauke da mutane 20 a lokacin da hatsarin ya auku.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya ba da umarnin a yi bincike kan hatsarin jirgin ruwa a Kwara

Ya ce an ajiye gawarwakin waɗanda suka mutu a ɗakin ajiyar gawa na asibitin jihar da ke Oyo.

“Bas ɗin, ɗauke da dukkan fasinjoji maza na tafiya zuwa yankin arewacin ƙasar lokacin da hatsarin ya auku,” in ji shi.

“An tsara bas ɗin don ɗaukar fasinjoji 14, amma an yi lodin fasinjoji 20,” in ji shi.

Mista Olugbesan ya yi ƙira ga masu amfani da hanyar da su yi taka tsantsan yayin tuƙi, da kuma gudun wuce gona da iri da kuma tafiye-tafiyen dare.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

4 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...